Karfe a wuta Hausa Novel Complete
ƘARFE A WUTA🔥*⚔️
MALLAKAR AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
MIKIYA WRITER’S ASSOCIATION
*BRIGHT PENS SECOND BATCH*
Writer of
Gaba da gabanta
Ƙanwar maza
Cutarwa
Ruɗin ƙuruciya
Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp:
*BISIMILLAHIRAHMANIRAHIM*
*Labarin ƙarfe a wuta, ƙirƙirarran labari ne, idan yayi kamanceceniya da rayuwar wani ko wata, arashi ne.*
Ban lamunci a juya mini littafi, ta kowace irin siga ba, sai da izinina❗
Page 1
Tsit ƙaton falon yayi, ba ka jin sautin komai, sai ƙarar gudun AC.
Sai mutanen falon da suke tsaye sun yi cirko-cirko, kamar masu jiran wani sakamako.
Wata matashiyar budurwa ce, durƙushe a kan gwiwoyinta, fuskarta ɗauke da wani yanayi na tsantsar damuwa, da tashin hankali, fuskarta tayi sharkaf da hawaye.
“Yanzu sakamakona kenan a wurinki? Irin wannan sakamakon shi na cancanta daga gare ki ko?”
Cikin ƙulewa wata babbar mace ta ce “Dama wani sakamako ka ke saka ran samu daga tsintaccaiyar mage? Ai ba za ta taɓa mage ba, abun da na din ga ankarar da kai kenan, tun a shekarun baya, amma ka kasa ankarewa, yanzu ta nuna maka ita ƴar kunama ce”
Budurwar ta yakice gumin da yake tsatstsafo mata, ba tare da nadamar abubuwan da suke gudana ba a ƙasan ranta, a zahiri ta ce “Ba mummunan sakamako bane ba, abun da ka tarbiyantar da ni a kai ne, gaskiya ita nake tsaye a kai, bani da niyyar cutar da kowa a gidan nan, kowa aikinsa yake yi, yakamata ayi mini adalci, ba a goyi bayansa a nuna ni ce nake kan ƙarya ba, a bari nima na yi nawa aikin”
Cikin tsawa ɗaya matar ta ce “Har wata gaskiya ce da ke…..
Dattijon ya ɗaga mata hannu ya ce “Ya isa haka, tashi ki je, ba na ko son ganinki, ki je ki yi abun da ki ke ganin ya dace da ke”.
Cikin rauni da tashin hankali ta ce “Abba, ba ka son ganina ka ce?”
“Eh mana, idan har ki na gudun ɓacin raina da fushina, dole ki ba wa ɗan uwanki duk wani cikakken haɗin kai, domin gudanar da aikinsa yadda yakamata”
Cikin matsanancin tashin hankali ta ce “Amma Abba ni kuma menene makomata…? Yakamata a ji ta bakina Abba”
Bai tsaya sauraron mai za ta ce ba, yayi gaba zai bar falon. Cikin matsanancin tashin hankali, ta riƙe ƙafarsa ta na fashewa da kuka.
“Haba Abbana, me yayi mini saura a duniya, idan har zan rayu ka na fushi da ni, ka yi haƙuri zan yi abun da ka ce in sha Allah” tuni hawaye ya cigaba da wanke mata fuska, tsantsar nadama da damuwa suka mamayeta, ta din ga kuka da sheshsheƙa kamar ta shiɗe, amma ya fizge ƙafarsa ya yi gaba.
Yana barin falon, tamkar mutanen falon za su cinyeta ɗanya, haka suka yo kanta sa surutu, kowa da abun da yake faɗa.
Tashi ta yi tsaye, ta goge hawayenta, cikin ko in kula, ita ma ta bi wata hanyar ta bar musu falon, cikin sigar kwa ci kanku.
Ɗakinta, ta shiga ta buɗe drower, ta fito da wasu takardu ta zube su a kan gado, ta kunna system ɗin ta da take caji a gefen gadon, lokaci guda kuma ta ɗauki wayarta tana dannawa.
Jin motsin mutum a bayanta, ya sanya ta waiwaya da sauri.
A tsaye ta ganshi bakin ƙofa, fuskarsa babu walwala balle annuri.
Mayar da hankali ta yi, za ta cigaba da danna wayarta, ya tako zuwa gabanta, ya tsaya ya ƙare mata kallo sannan ya ce “Kin shirya aikata abun da aka umarce ki ko kuwa?”
Cikin hanzari ta tari numfashin sa ta ce “Ban ce shirya ba, kuma ba zan shirya ba, daga nan har gaban abada, ka fita ka rabu da ni”.
Cikin matuƙar mamaki yake bin ta da kallo, “Yanzu duk kukan da ki ka yi, ƙarya ki ke yi kenan?”
A hasale ta ce “Ina ruwanka, idan ma kukan ƙarya ne ko na gaske, ka yi aikinka in yi nawa, kar ka sake yinƙurin shigar mini aiki, idan ba haka ba komai yana iya faruwa, wallahi ba zan fasa abun da na yi niyya ba, idan kuma ka cigaba da takura mini, zan baka mamaki”
Hannu ya saka, ya ɗagota daga kan gadon ya ce “Menene zai faru, wani irin mamaki zaki bani? Me zai faru nake son ki gaya mini. Kina da hankali kuwa? Kin san doka amma kina taka ta yadda ki ke so? Da me ki ke taƙama ne haka?”
“Doka ko? Ni iya takata na yi, kai kuma cin zarafinta ka ke ƙoƙarin yi, ka ƙyale ni babu ruwanka da ni, ka yi naka aikin na yi nawa duk wanda yayi galaba shikenan. Idan ka ga dama ka je ka sake gayawa Abba abun da duk yayi maka a kaina, wallahi babu gudu babu ja da baya, ban fara dan ina saka ran dainawa ba, ba tare da na yi nasara ba” hankaɗata yayi kan gadon, yana wani irin huci, zuciyarsa na yi masa zafi, yayi wata irin ƙwafa yana bin ta da kallo. Cikin hanzari ya fice ya bar mata ɗakin, saboda idan ya cigaba da tsayuwa, zai iya yi mata abun da ba shikenan ba. Ta yinƙura ta tashi zaune tana haki, tana kallon ƙofar da ya fita.
****
Tsaye take a gefen wani gini, tana ƙarewa harabar kotun ido. Yadda aka cika harabar da manya da ƙananan motoci ne, ya sake tabattar mata da manyan shari’oi za a gudanar a yau.
Ta din ga kallon agogon hannunta, tana kallon gate shigowa harabar kotun.
Motar gidan yari ce ta shigo, aka yi parking ɗin ta, sai dai tsayuwar motar babu daɗewa wata danƙareriyar motar, ta shigo harabar kotun.
A ƙalla an kai mintuna goma da parking ɗin motar, sannan aka buɗe bayan motar, wata mata ta fito, sanye cikin coat.
Mutanen da ke harabar wurin, suka nufeta, wasu suka karɓi jakarta, ana ta yi mata fadanci, cikin girmamawa.
“Ya Allah kai ne Allah, kai ne buwayi gagara misali, Ubangiji da babu wani kafinsa, kuma babu wani a bayansa. Allah na san mutanen nan sun fi ƙarfina ta ko ina, amma kaine abun dogaro na, na san ba za ka bani kunya ba. Allah sun fi ƙarfina ka fi mini ƙarfinsu. Allah ka yi mini kunfayakununka a kan shari’ar nan, hasken gaskiya ya shafe duhun ƙarya, duk da ina da masu goya mini baya, amma Allah goyon bayanka nake buƙata” ta jima a tsaye tana karanto addu’a, tare da yi wa Allah kirari.
A hankali ta furta “What a hectic trial, Ubangiji ka iya mini” cikin nutsuwa, ta fara taka takalminta mai tudu, ta nufi shiga cikin kotun, da takunta mai kama da na ƙasaita, shigarta ta lawyoyi tayi matuƙar yi mata kyau, tana tunkarar ƙofar shiga, zuciyarta na tsananta bugawa,tana fatan Allah ya shiga lamarin ta.
****
Ƙofar famfo kano state.
Ƙarfe goma saura mintuna goma na dare, tuƙi yake yi cikin sauri, saboda yadda fasinjar da ya ɗaukko take azalzalar sa. Duk saurin da yake yi, mita take yi masa, a kan ya ƙara gudu.
Yanayin kwalliyar da ta yi, cikin baƙin material, fuskarta ta sha make-up, zai tabattar maka daga wurin biki take.
Ta kalli agogon hannunta, kamar ta fashe da kuka ta ce “Mai napep, ka yi wa girman Allah ka yi sauri”
Ya ce “Wai dan Allah hajiya yaya ki ke so na yi ne? Haba babata duk saurin da nake yi, ki yi haƙuri mana mu tafi a sannu”.
A ƙule ta ce “Ban gane babarka ba, wani irin wulaƙanci ne wata babarka, na yi maka kama da tsohuwa ne?”
Yayi murmushi ya ce “A’a, ai ku mata duk in da ku ke iyaye ne… Katse shi ta yi ta hanyar cewa “kuma sai aka ce na haifi kamar ka? Ai sai a bari na haifa tukuna, a yanzu na haifi kamar ka, ai tawa ta ƙare a duniya. Ko yayarka ka ce mini ka cuce ni, balle babarka. Ni dai ka ƙara sauri, yau na san kashina ya bushe, sai an yagalgalani da masifa a gida yau. Aikin banza, ƙawayen amarya ƴan wahala, mun gama wannan wahalar a ɗauke ta a mota an kai ta gidanta, mu muna fama a titi. Mu ma Allah ya kawo lokaci, ace ga miji ga mota”
Ya waiwaya ya kalleta yana murmushi, a fusace ta ce “Lafiya malam?”
“A’a Allah ya baki haƙuri”.
Kafin su ƙarasa in da zata sauka, ta ciro masa kuɗinsa, su na zuwa in da za ta sauka, ta miƙa masa, ta sauka tayi cikin layinsu da gudu a kan takalminta mai shegen tsini, ko wahalar gudun ba ta ji.
Mayafinta da jakarta a hannu, ta tura gate ɗin ta shiga ta na haki.
Wani matashin saurayi, yana tsaye a harabar gidan hannunsa riƙe da waya, ya kalleta ya ce “Daga ina ki ke?”
“Biki” ta bashi amsa kai tsaye.
“Za ki ci ubanki kuwa, Major yana nan ido biyu, tun ƙarfe takwas ya dawo yake tambaya ko kin dawo, gashi kin kashe waya ke ga ƙwararriya”
Cikin ta yayi wata ƙara saboda tsoro “Allahumma inni as’aluka afuwa wal afiya, yau na kaɗe” ta ƙarasa maganar tana nufar cikin gidan.
Cikin sanɗa ta shiga falon, sai dai tana shiga, ta fara tozali da dattijon zaune a kan kujera 3 seater, ya sanya ƙofar shigowa falon a gaba, da gani babu tambaya ta san ita yake jira.
Tsayawa tayi ƙyam da takalmanta a hannu, da jaka da mayafi, kamar ta juya da gudu ta koma.
“Daga ina?” Yayi mata magana cikin dakakkiyar muryarsa.
Cikin rawar murya ta ce “Abba, wurin biki”
“To juya ki koma in da ki ka fito”
“Ai an tashi” tayi maganar kamar ta fasa ihu, dan tuhumar Abba babu daɗi.
“Dama haka mu ka yi da ke? Ki fita ki je ki yi zamanki? Ki dawo mini gida bayan goma, sai ka ce ki na zaman kanki?, koma ki kwana a in da aka yi bikin”
“Dan Allah Abb..”
“Get out, kar ki kuskura ki yi mini magiya. Duk gidan nan babu mai bani ciwon kan da ki ke bani Arfa, koma in da ki ka fito ba ki da wurin kwana a cikin gidan nan yau” da gudu ta juya ta fita saboda tsorata da ta yi.
Ta koma harabar gidan, a ƙasan zuciyarta ta ce “Na shiga uku, ni ake kora kamar wata karya, yanzu idan gidan mijina ne, ba sai dai ya gama bala’in in shige ɗaki na bar shi ba..
Ba ta gama tsinkewa da lamarin ba, sai da major ya kulle babbar ƙofar shiga cikin gidan.
Ta zube kayanta, ta tafi famfon harabar gidan, ta dinga wanke fuskarta, ta wanke kwalliyar fuskar gaba ɗaya, ta koma ta zauna jiran tsammani ko Allah zai saka Abba ya buɗe mata ƙofa.
Samarin gidan suka fara fitowa daga BQ, suna shimfiɗa a harabar gidan, za su yi kwanciyar zafi. Sai wulaƙanci suke yi mata, suna yi mata Allah ya ƙara, suna kyararta, kamar wadda ta aikata wani gagarumin abun kunya.
Ganin ba ta da mafita, ta laluba ta samo tabarma ta shimfiɗa, ta yi kwanciyarta dan a gajiye take sosai.
Tsakar dare, ta yi juyi, ta ji babu kowa a kan gadon sai ita kaɗai, mamaki ya kamata, ta kalli agogon wayarta, biyu da rabi na dare.
Tasowa ta yi ta fito nemansa, sai dai ga mamakinta, ta tarar da shi a ventilation ɗin saman bene, ya zauna a kan kujera ya saka harabar gidan a gaba, hannunsa riƙe da ɗan ƙaramin Alqur’ani yana karantawa.
“Lafiya dai?” Tayi maganar cikin mamaki.
Ya waiwaya ya kalleta ya ce “Lafiya ƙalau”
“Amma me ka ke yi a wurin nan, a wannan uban daren? Na zata tuni ka kwanta, na fito na duba falo baka nan”
Cikin ko in kula ya ce “Kar ki damu, ki je ki yi kwanciyar ki, Arfat ke punishment”
Cikin takaici matar ta ce “To ta na punishment, sai kuma kai ka zo nan ka zauna, ka hana idonka bacci?”
Yayi murmushi ya ce “Ko na kwanta ba zan iya rintsawa ba, ki yi kwanciyar ki kawai” tamkar ta yi tsaki, haka ta wuce shi ta ƙyale shi, tama tunanin yaushe ƙarshen wannan lamarin zai zo?.
Haka ya kwana a zaune, yana gadin harabar gidan, duk wanda yayi juyi cikin mazan nan, yana kallon shi.
Yana ganin yadda Arfa ke ta juyi, sauro ya dame ta, sai da ya ji tamkar ya sauka ya samu abu ya rufe ta, amma ya ƙyale ta.
Asubar fari, ya yi alwala, ya sauka ƙasa domin tafiya masallaci.
Samarin na jin takunsa, suka din ga tashi, idan ba haka ba, ya tashi mutum da carbi.
Ya na zuwa in da take kwance tana bacci, ya tsula mata carbi a ƙafafuwanta.
A razane ta tashi tana rarraba ido.
Bai ce mata uffan ba, ya yi gaba ya fice.
Tana ganin ya fita, ta tattara komatsanta, ta shiga cikin gidan, sai soshe-soshe take yi, saboda uban sauron da ya cije ta.
Cikin ɗakinta ta shiga, ta watsar da jakarta da sauran kayan a kan gadonta, ta jona wayarta a caji.
Ta tuɓe kayanta daga ita sai underwear. Wata matashiyar budurwa da aƙalla za ta ɗan girmewa Arfa ta fito daga banɗaki, ta kalle ta, ta ce “Arfa, ke kuwa a ina ki ka kwana? Har sha ɗayan dare ba ki dawo ba” banza tayi mata, ta taho fuuu ta kusa bangajeta, ta shiga banɗaki. Ta girgiza kai kawai ta shimfiɗa sallaya.
Da ƙyar ta yi sallar asuba, sai soshe-soshe take yi, tana idarwa ta ɓingire ta hau bacci a wurin.
Sosai take baccinta, dan ta gaji sosai, ga baccin jiya sam bai yi mata daɗi ba.
“Nabila!Nabila!!”
Tsaki tayi tare da jan “Innalillahi wa Innalillahi raji’un, menene, wannan wane irin kira ne dan Allah?”
“Abba ne ya ce, ace miki yana fatan kin ajiye aiki ne, da ki ka kwanta kina bacci haryanzu ba ki fita ba”da sauri ta buɗe idonta, gaba ɗaya ta manta yau Monday.
Kamar korarriya ta tashi, ta afka banɗaki, a gurguje ta wanke bakinta, tayi wanka, ta fito ta shafa mayuka, da turaruka ta shirya cikin uniform.
Ta saɓa coat ɗin ta a kafaɗa, ta ɗauki jakarta ta goyo, ta sanya takalminta, tayi waje tana kunna wayarta.
Ta shiga kitchen, ta buɗe fridge ta ɗebi lemuka ta zuba a jakartab, da abun da ta ajiye da wanda ba ta ajiye ba, duk ta kwasa ta zuba, ta zuge jakar ta fito falo.
A falon suka yi karo da wata matashiyar mata, matar ta kalli Nabila ta ce “Ma’aikaciya ko mahaukaciya, kalleki kamar korarriya Nabila, zaki fita aiki amma ki ka kwanta ki na kwasar bacci abinki”.
Nabila ta ce “Anty, the whole barrister ki ke cewa mahaukaciya?”
“Yo banda shirme, kalleki kamar an hankaɗoki, ke wannan wane nutsatstsen ne ma zai ce ki tsaya masa shari’a?”
Nabila ta ce “I will fill a lawsuit against you, what you did is deformation of character, the whole barrister Anty ki ka zaga”
“Wuce ki tafi kafin na make ki ni? Idan suka kore ki daga wurin aikin, ai kya nutsu” Nabila ta sake kwasa da gudu a kan takalmanta kamar ba budurwa ba.
Mai aikinsu ta tarar a famfon harabar gidan, tana wanke-wanke.
“Shalelen Abbanta, yau kamar kin makara”
Ɗaga mata hannu kawai Nabila ta yi, kowa ya ganta sai yayi magana, ta kalli hanyar benen Abba, kamar ta je ta gaishe shi, amma ta fasa ta san yadda ta makaran nan, sai ya zaunar da ita yayi mata faɗa, ga laifin jiya ga na yau, kuma ta san sai ya haɗa har da na waccan shekarar yayi mata, dan haka tayi wuf ta fice waje.
Duk irin vibration ɗin da wayarta take yi, ba ta ɗaga ba sai da ta zauna a cikin adaidaita sahu, sannan ta ɗaga kai wayar kunnenta.
“Wai Nabila wani irin wulaƙanci ne, nake ta kiranki ki ka ƙi ɗagawa?”
Nabila ta ce “Ke ban son tijara, kin wuce aiki ne?”
A fusace mai maganar ta ce “Ban sani ba”
Nabila ta yi dariya ta ce “Sorry masoyiyya, ki fito titi gani nan” tafiyar mintuna sha biyar suka yi, suka iske wata matashiyar budurwar a titi, sanye cikin doguwar rigar abaya, ta kama adaidaita sahun ta shiga tana hararar Nabila.
“Sorry sumy, kar ki fashe dan Allah”
“Wallahi kin fusata ni Nabila”
“Shiyasa na ce ki yi haƙuri ai, ya gidan ya su mama?”
Sumayya ta ce “Suna lafiya ƙalau, meyasamu fuskarki? Na ga kamar ƙuraje”
Nabila ta rausayar da kai ta ce “Ke bari, the whole me, jiya Abba ya saka na kwana a haraba, sauron nan na cikin flowers suka yi idi a kaina”
Sumayya ta waro ido ta ce “Wai da gaske?”
“Zan yi miki ƙarya ne? Wallahi dattijon nan ya ce wai na koma in da na fito ya rufe ƙofa. Aikuwa na din ga tsinewa amaryar nan, na baro ta a gidanta cikin nishaɗi da farinciki, ni kuma na afka tashin hankali, kamar ni degree holder, Abba ya rufewa gida. Yanzu dan Allah da a gidan mijina ne, da ba sai dai yayi masifar ya gama ba, babu wanda ya ji ya gani? Ai Abba ya tozarta ni jiya. Sai so ake a ga fuska a tuhume ni, ko ayi mini rashin mutunci a gidan nan, kin san gidanmu Allah ya wadata mu da munafukai, ni kuwa na haɗe rai”
Sumayya ta ce “Allah ya ƙara, ke uwar gwaninta, har da kai amarya, banda uban anko da ki ka yi mata. Ina mai tabattar miki ke da ganinta ta tako gidanku, sai wani ikon Allah”
Nabila ta ɗan yi shiru ta ce “Ku ma fa haka ne, kin san wani abu, ba hassada nake yi wa amira ta yi aure ba, amma kalli na fita kyau fa, na fita komai amma amira ta shige daga ciki, ohh ni Nabila, duk kyan nan da dirin nan yadda ki ka san na je na haye kan high table ɗin nan ayi da ni ranar dinner. Ba ma wannan ba duk wannan gayun da kwalliyar ban yi saurayi a bikin nan ba”
Sumayya ta ce “Ki je ki ɗorawa ranki jarabar son aure, ki ƙi focusing a kan career ki, ni ko a jikina na san lokaci ne, kuma tun da ba yawon iskanci nake ba, duk wadda ta yi mini gorin aure sai na ci ubanta, shekarun namu nawa ne duka da za a addaba mana”
Nabila ta yi ajiyar zuciya ta ce “Ba haka ba ne Sumayya, we have a different backgrounds, ke kin san me nake nufi, wallahi ƴanci nake so Sumayya, ko ta halin ƙaƙa”
Sumayya ta ce “Kar neman ƴanci ya kai ki ga halaka, duk ina samarin naki ne to?ba wanda zaki tsayar?”
Zafin Kai Hausa Novel Complete
Nabila ta yi tsaki ta ce “Bar matsiyata, daga ƴan wahala sai ƴan iska. Sai dai duk wanda ya zo hannuna sai na ci rabona ayi baran-baran. Na daina wahalar son mutum, daga ƙarshe yayi breaking heart ɗina, ya ci bulus. And also haryanzu ban samu spec ɗi na ba kin dai gane”
Sumayya ta ce “Au ke yanzu har wane zaɓe-zaɓe ki ke yi?”
Nabila ta ce “To ana raba mai rai da motsi ne? Iya wuya akwai abun da zuciya take so, kuma ni na fi son namiji mai kumari sosai. Irin wanda zaki ganshi ingarman namiji mai cikar zati. Beside fuskar namiji ba gemu, ai sunansa sumayya, ni kuma daga dattijai, sai marasa gemu, sai kuma ƴan wahala, ni matashi nake so, ba kuma yaro ba”
Sumayya ta ce “Au sunana ne ma abun kwatancen iya shegenki ko, to ki je dan kanki. Mai napep zan sauka a nan, za ta baka kuɗin”
Nabila ta ce “Ke uban waye ya ce miki ina da kuɗi?” Tuni Sumayya ta sauka, ta bar Nabila.
Nabila ta yi ƙwafa ta ce “Zamu haɗu ne, zaki ga wulaƙanci”.
***
A hankali yake buɗe jajayen idanunsa, a lokaci guda kuma yana lumshe su, tamkar mai shirin yin bacci. Sai mirgina kansa yake yi, yana sake lumshe manyan idanunsa da suka koma jajaye matuƙa.
Tamkar an jefo shi, haka ya faɗo ɗakin, yana rarraba ido.
A hankali ya ɗaga kai ya kalli wanda ya shigo ɗin, ya mayar da kansa ƙasa ya sunkuyar.
“Allah ya taimaki oga…” Bai amsa ba kawai ya buɗe tafin hannunsa ya miƙa masa.
Wata baƙar leda ya ciro, ya ɗora masa a hannun, sannan ya ce “Sai dai Oga ba a samu da yawa ba, ƴar kaɗan ce, cinnaku sun yi wa kasuwar ƙawanya, shiga da fitar kaya na bayar da wahala, da ƙyar na samu wannan wurin wani ɗan inyamura, ina ga wuri zan canza, saboda kamar ana son yi mini cune”.
Bai ce masa uffan ba, ya kwance ledar, ya fito da kwalin wata allura pack guda, mai ɗauke da ampoule na allura guda goma.
Sirinji lamba biyar ya ɗauka, ya din ga fasa alluran yana zuƙa, sai da ya cika sirinjin, sannan ya miƙe hannunsa.
Ya ɗaga kansa ya kalli matashin da ya kawo masa allurar, bai ce masa komai ba, matashin ya bar ɗakin.
Ya mayar da idonsa kan hannunsa, ya yana kallon jijiyoyin da suka kwanta ɗoɗar a ƙarƙashin fatarsa, suka yi ruɗu-ruɗu, manya da ƙanana.
Ya dubi guda ɗaya, ya huda ta da sirinjin hannunsa, ya fara bawa kansa allurar sannu a hankali. Sai da ya zuba ta duka, sannan ya yi jifa da sirinjin, ya sunkuyar da kansa ya na jiran Sakamakon hukuncin da ya ɗauka.
Sai dai kusan mintuna goma sha biyar, bai ji abun da yake so ba, sai wani irin nauyi da kansa ya ƙara, idonsa ya din ga yi masa yaji, ya rintse idanunsa amma bai ji alamar abun da yake so ba.
Abu kamar wasa kansa ya din ga wani irin sarawa, ƙirjinsa yana zafi. Ya dafe kansa da hannunsa bibbiyu yana jujjuyawa tare da rufe idanunsa.
Ihu ya fara yi iya ƙarfin sa yana taƙarƙrewa, yana girgiza kansa, saboda yadda yake jin kansa tamkar zai yi bindiga.
Da gudu suka shiga ɗakin, suka fara ƙoƙarin danne shi, amma ya yi ihu ya watsar da su baki ɗaya ya cigaba da kururuwa.
Ayshercool.
08081012143
[8/29, 8:34 PM] Halimatu A/Rahman Sadeeya:
⚔️*ƘARFE A WUTA*⚔️
MALLAKAR AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
MIKIYA WRITER’S ASSOCIATION
*BRIGHT PENS SECOND BATCH*
Arewabooks ayshercool7724
Watpad ayshercool7724
2
A ƙalla sun kai ƙarti uku majiya ƙarfi, suka riƙe shi, amma sai ƙoƙarin watsar da su yake yi, ga wani irin gurnani yana yi, kamar mahaukacin zaki.
Da ƙyar suka haɗu suka kai shi ƙasa, suka daddane shi yana cigaba da ƙoƙarin watsar da su ya tashi.
Ɗaya daga cikinsu da yanayin kamanninsa ya bayyana, ƙarara shaye-shaye ya huda shi, saboda yadda laɓɓansa suke baƙi ƙirin, ga wani irin ƙaton tabo a gefen fuskarsa.
A hankali yake ɗan dukan bayansa cikin sigar rarrashi yana faɗin “Easy maza, easy, mun san ka na cikin damuwa da raɗaɗi, amma hakan ba mafita bane ba, ka yi haƙuri muna tare da kai ɗari bisa ɗari iya wuya” ya cigaba da maganar yana rarrashin sa.
A hankali jikinsa ya saki, ya daina gurnanin da yake yi, ya lumshe idanunsa, ya rufe su, tamkar mai bacci. Sai da suka tabattar ya yi relaxing, sannan suka ɗaga shi.
Major ne tsaye a gaban mudubi, yana ƙara kintsa jikinsa kamar wani matashi, ba dattijo ba, uwargidan sa na gefensa tana taimaka masa yana shiryawa, Ba tare da ya kalle ta ba ya ce “Arfa kuwa ta tafi aikin?”.
Ta yamutsa fuska ta ce “Ta ga dama ta tafi”
Ya jinjina kai ya ce “Punishment ɗin da na yi mata jiya, shi ya hana ta zo ta gaishe ni yau kenan,’? zan gamu da ita ne idan ta dawo”.
“Dan girman Allah major ka ƙyale sabgar yarinyar nan, sai ka ce itakaɗai ce ƴa a gidan nan, komai ita su duk sauran ba ƴaƴa bane ba, da ba ka damu da lamarinsu ba?” Kallon da yayi mata ne ya sanya ta yin shiru, tare da sunkuyar da kai, bai sake ce mata komai ba, ya ɗauki mukullin motarsa ya fice.
Cike da takaici ta sauka daga benen, ta fito main falon gidan tana mita.
“Yaya ya dai? Meyafaru ne?” Duk da ba ta kasance mai sakarwa abokan zamanta fuska ba, amma haka kurum ta tsinci kanta da gaya mata abun da ya faru saboda takaici.
“Major ne mana, gaba ɗaya ya tattara hankalinsa a kan yarinyar nan, kamar itakaɗai ce ƴa a cikin gidan nan, jiya kwana na ne, amma a barandarsa ya ƙare kwanan jiya, wai yana gadinta, abubuwan nan sun fara isata”
Ɗayar ta taɓe baki ta ce “Ai ni na gaji, na zuba ido su ƙarata, abun da ba jiya aka fara ba, ba yau ba”.
Anty, wadda take ta uku, da take karyawa, duk da ba da ita suke ba ta ce “Amma dai an yi abun kunya, kishi zan ce ko baƙin ciki da ƴar cikinku”
A fusace Uwargidan major, da ake cewa Mama ta ce “Asiya, da ni ki ke ko wa?”
Anty ta ce “Duk wanda ya tsargu, sai menene dan ya nuna mata kulawa ta musamman, duk kulawar da yake bawa sauran yaran bai isa ba? Ƴaƴa nawa ne a gidan nan, kowanne ya na bashi kulawa dai-dai da buƙatarsa ne, amma da yake kishi ya zame muku bala’i, mussaman ma ke, da kowa ma yi ki ke, kin fi mu daɗewa da shi, amma haryanzu ba ki san halinsa ba”
Mama ta ce “Ba zan yi musayar yawu da ke ba ƙanwar bayana, dan ba ki isa ba, da wanda ya ajiye ki zan yi”.
Anty ta ce “Idan ma ƴar cikinki ce, matsayinmu ɗaya matan major, kuma ni gaskiya nake faɗa” haka suka cigaba da ƴan faɗace-faɗacen su na kishi.
Nabila kuwa da wasu lokutan a kan yi mata laƙabi da Arfat, tana zaune a katafaren office, itakaɗai sai aikin danna waya take yi, cikin nishaɗi kamar babu wani abu da yake damunta.
Knocking ɗin ƙofar office ɗin aka yi, ta bayar da izinin a shigo.
Nabila suka gaisa da matar ta ce “Nabila ko?”
Nabila ta jinjina kai ta ce “Eh”
“Ki zo Barrister yana kiranki”
“Wane barrister?”
Matar ta ce “Director. Dama ina son in yi miki magana. Kin ga wurin nan babbar organization ce, da muke dealing da mutane daban-daban, especially manyan mutane. Yana da kyau ki jajirce director baya son ragwanci ko harkar ko in kula da aiki, sai ku samu saɓani”
Nabila ta yi murmushi ta ce “Na gane, na kuma fahimta na gode sosai” matar ta jinjina kai ta fita.
Nabila ma tashi ta yi, ta fita ta tafi office ɗin da ake nemanta.
Ta tarar da shi da wani babban mutum a zaune a office ɗin sa, ta gaishe su cikin girmamawa sannan ta kalli Director ta ce “Sir gani”
Ya kashingiɗa ya ƙare mata kallo sannan ya ce “Nabila, what is actually wrong with you ne?”
Cikin mamaki ta ce “Ni kuma? Me na yi sir?”
Ya gyara zamansa ya ce “Anya ke ki ke son zama lawyer ko choice ɗin major ne? Tun da ki ka zo wurin nan you don’t care, sai dai ki zauna ki danna waya, ki yi ciye-ciye, sai kwalliya. Bama kya shiga cikin ma’aikatan ki ga yadda ake aiki, balle mu ga gogewarki, mu faa tura ki trials, dama zuba miki ido na yi amma na ga baki san zuru ba” Nabila ta yi shiru ta sunkuyar da kanta ƙasa.
“Ina buƙatar ganin canji a tare da ke, idan ba haka ba na fara kai ƙarar ki wurin Major, yanzu muna da client da yake son yin apeal, a kan wata shari’a da wasu mutane suka kai ƙararsa. Ki je na saka ki a team ɗin su barrister Habib, ki je ku tattauna yadda za ayi handling case ɗin. Effort ɗinki shi zai sanya na baki manyan cases to help your career”
Ta risunar da kai ta ce “Ok sir” ta juya ta fara tafiya, sai dai mutumin da tarar a office ɗin, ya bi bayanta da kallo yadda ƙugunta ke juyawa, cikin skirt ɗin kayan jikinta.
Office ɗin Barrister Habib ta je, aka sanar da ita suna ɗakin sirri, dan haka kai tsaye can ta wuce.
Ta tura ƙofar ta yi sallama, suka amsa mata, ta nemi wuri ta zauna.
Barrister Habib ya ce “Kin ga damar zuwa kenan?” Wani irin kallo ta yi masa, amma ba ta ce komai ba, su kuma suka cigaba da abun da suke yi.
Shari’a ce a kan wani attajirin mutumin ya karɓe gonakin wasu ƴan ƙauye, ya basu diyya ya fara ginin kamfanin sarrafa shinkafa, sai dai suka yi ƙararsa diyyar da ya biya su, ta saɓawa yarjejeniyar da suka yi da shi, dan sam bai kai darajar gonakinsu ba. Ganin ba su da galihu, ya sanya bai damu da ƙarar da suka kai shi ba, sai da aka yanke hukuncin ya biya su, sannan ya ce zai yi apeal.
Mamaki ya cika Nabila, irin maƙudan kuɗin da ya biya law firm ɗin su, a bashi lawyoyi su kare shi, ya isa ya ƙarawa mutanen nan, ya biya su haƙƙoƙin su.
Nabila dai ta yi zuru da ido, tana kallon yadda ake harhaɗa hujjoji na halal da na haram, domin mutumin yayi nasara a kotu.
Baƙin ciki da takaici suka isheta, sunan ƙauyen da abun ya faru kawai ya isa ka gane cewar masu ƙaramin ƙarfi ne. Dan galibi mutanen karaka da Allah suka dogara, da harkar noma suka dogara.
Tashi ta yi tsaye ta ce “Excuse me please, na fara jin yunwa lokacin cin abincina yayi”
Duka lawyoyin da shi kansa client ɗin suka ɗago suka kalleta.
Habib ya ce “Ana tsaka da aikin?”
Ta basar ta ce”Am sorry, am having a chronic ulcer, za a iya samun matsala, idan na cigaba da zama” daga haka ta ɗauki jakarta ta fice, tana mitar ba zata zauna a ƙulla wannan sharrin da ita ba, ranar lahira ta shiga uku.
Ta koma office ɗin ta, ta yi alwala tayi sallar azahar, ta je ta samu Director ta sanar masa da tana da uzuri ta na son ta tafi, yayi mata iznin hakan.
A hanya ta tsayar da mai napep, suka ɗauki sumayya, sannan suka tafi.
Ta kalli Sumayya ta ce “Sumy, meyafaru ne? Na ga kina wani ɓata rai”
Sumayya ta yi tsaki ta ce “Haushin kaina nake ji, da na karanci aikin jarida Arfa”
Cikin mamaki ta ce “Amma meyasa, na ga shi ne zaɓinki?”
“Wallahi duk ya fita daga kaina, hira aka yi da honorable Indabo, wai an yi borehole a ƙananan Hukumomin da yake wakilta, an raba kayan makaranta ga ɗalibai. An kai bencina makarantun firamare da na islamiyyu. Last week aka ce na je na tattauna da al’umman local government ɗin, na je ni ban ga ayyukan da aka yi ba, na tattauna da mutanen ƙananan hukumomin, sun ce ba ayi musu ba. Na kai recording ɗin, aka saka, wai lawisa ba ta tantance shirin ba, ba ta sani ba aka saka, kin ga cin mutuncin da aka yi mini, wai zan lalata musu business wai sai na je na samo mutanen da zan yi hira da su, su ce eh an yi ayyukan su yi godiya alhalin ba ayi ba. Na zama maƙaryaciya kenan me zan ce wa Allah? Wai har da idan ban yi wasa ba, sai honorable ya saka an ɗaure ni”
Nabila ta ce “Ikon Allah, ashe duk kanwar ja ce sumy, yo nima hakan take ai, wani tasonon Alhaji ne ya zo yayi kirim a kan kujera kamar damin doya, ya biya uban kuɗi wai za a kare shi, ya cuci talakawa ko kunya bai ji ba, kuma director ya sakani a team ɗin lauyoyin, ni dai ba zan yi ba wallahi, sai dai ya yi ta gaya wa Abban. Haka kurum a cuci mutane ka je ka cewa Allah me?”
“Wallahi Nabila, ba ki ji zuciyata ba, yanzu sai dai na je na tara maƙwabta na yi hirar ƙarya da su, a zo a sake sakawa, kuma wai sai na rubuta takardar ban haƙuri, ki ji fa”
Nabila ta ce “Tirƙashi, wai ya ɗaure ki, to ya ɗaure ki shi ma ya hau da ɗaurin Allah ” Haka suka cigaba da tattaunawa, har suka isa in da sumayya za ta sauka.
***
Cikin tsananin tashin hankali, yake magana, kallo ɗaya zaka yi masa ka san hankalinsa a matuƙar tashe yake.
Ya daki teburi ya ce “Kwamishina, dole fa ku nemo yaron nan, dole ku mayar da hankali a nemo shi a duk in da yake a ƙasar nan”
Mutumin da yake zaune cikin kakin ƴan sanda ya ce “Honorable, ka kwantar da hankalinka, aikinmu baya buƙatar garaje da gaggawa, sai mun bi a sannu”
“Haba Cp, wane irin bi a sannu? Rayuwata na cikin hatsari, yayi iƙirarin kashe ni, dole fa a nemo yaron nan, ko be kashe ni ba, idan ya buɗe bakinsa yayi wata magana a kaina kashina fa ya riga ya gama bushewa, na san fa waye yaron nan ciki da bai”
Cp ya gyara zamansa ya ce “Amma honorable, wace irin yadda ko alaƙa ce tsakanin ka da yaron nan, da har ya sanka haka, zamansa a gari yake barazana a gareka”
Tsaki mutumin yayi ya ce “Kai har ka tambayi alaƙar da ke tsakanin ɗan siyasa, da tantirin ɗan daba, ɗan iska? Ku nemo shi dillalin wiwi ne, da hard drugs. Da kun ganshi ma kawai a harbe shi, kuma a tuhumi controllern gidan yari, a kan dalilin sakinsa, bayan ko shari’a ba ayi masa ba tsawon lokaci”
Ɗan sandan ya jinjina kai ya ce “Shi controller ya ce court order ya karɓa”
“Ni dai ka yi mini wannan taimakon a nemo shi da gaggawa, dan yana cikin garin nan, tun da ga ayyukan ta’addanci yana ta yi yadda ya ga dama”.
CP ya ce “In sha Allah, ka kwantar da hankalinka za ayi duk mai yiwuwa, zan nemi zaƙaƙurai daga cikin mutanenmu, da suke dealing da criminal cases, very soon zai zo hannu, DSP Nasir na san zai yi abun da ya dace in sha Allah”
“Yauwwa to shikenan, ko dai sanarwa za ku yi, ace duk in da aka gano shi a kamo shi, an sake shi ba bisa ƙa’ida ba”
Da sauri ya ce “No ai ba haka aikin tsaro yake ba, ai wannan abun kunya ne ga hukumominmu, yanzu sanin in da yake shi ne babban target ɗinmu, dan yaron yana da wayo sosai, na bibiyi record ɗin sa, sai an yi taka tsantsan sosai wurin kama shi, sai an yi amfani da dabarun aiki, hatsabibi ne sosai”
“To ayi ƙoƙarin hakan dan Allah”.
***
Gudu-gudu sauri-sauri ta ƙarasa gida, saboda azababben fitsarin da ya cika mata mararta, tana zuwa ɗaki ta watsar da komai a kan gadonta, ta shiga banɗaki.
Sai da ta gama fitsarin, ta ji iska na shigarta, tayi wanka ta fito, ta tattare kayan da ta watsar, ta samu riga ta shan iska ta saka, ta shafa turare ta fita.
Kitchen ta shiga dan zuba abinci, ta ci karo da fate-faten wake a cikin food flask ɗin ta. A ƙule ta ja uban tsaki, ta fito babban falo kamar ta fashe da kuka, ta hau ƙwalawa mai aikinsu kira.
“Baba magajiya!”
Daga can wani sashen ta amsa da “Na’am, Arfa gani nan”
“Na ga faten wake yau?”
“Eh, umarnin Hajiya babba ne, ita ta ce ayi faten wake”.
Cikin ɗaga murya arfa ta ce “Amma dai an san ba na ci ko? Kin dafa mini wani abun ne?”
Magajiya ta ce “Wallahi har na ɗaukko doya na fara frayewa, na ɗan dafa miki, na soya miki miya, aka kuma sakani aiki”.
Nabila cikin kwakwazo take masifa “Saboda tsabar an tsane ni, so ake na mutu a huta, in je aiki in dawo a kasa ajiye mini abinci, sai a dafa abun da ba na so”
“Ke Nabila meye haka ne, hajiya ce ta bayar da umarnin hakan, ki shiga kitchen ki dafa wani abun mana” Nabila ta kalli Yaya Sauda ta ce “In je in dawo yanzu, sannan in shiga kitchen in hau girki, bari in je in sha faten waken, duk abun da ya same ni, ku kuka kasheni, ai kun san likita ya hana ni cin wake”
“To ki je ki ci ɗin mana, idan kin mutun sai ne? Banda gulma amma ai ki na cin ƙosai da shinkafa da wake, ko duk su ba waken bane ba”
Kamar ƴar goye, Nabila ta din ga zirarar da hawaye ta na bala’i.
“Kar Allah ya sa ki ci abun da aka dafa, kya mutu da yunwa agola ƴar wahala”.
Cikin tsananin fusata Nabila ta ce “Tun da dai ba shegiya ba ce ni da ubana, ai da sauƙi”
Cikin son kunna Nabila, Sauda ta ce “Meye marabarki da mara uban?”
Baba magajiya da ke tsaye ta ce “A’a Sauda, dan Allah kar ayi haka, ke fa babbace”
Sauda ta ɗaga mata hannu tare da cewa “Babu ruwanki, ki wuce ki ƙarasawa mama aikinta. Ke kuma ki tsaya ki cigaba da hauka, banda samun wuri ina na taɓa ganin agola da miƙe ƙafa”.
“Ai gara ni, agolar ce, kuma iya wuya ni ƴar gari ce, ba baƙuwar haure ba, jikar yarabawa. Kuma ni ba dan albarkacin ubana ba, wallahi da na daɗe da barin gidan nan, gara na je na kama gida na yi zaman kaina, iyaka ace ina zaman kaina, ba ɗan iskan da zai takura mini”
Sauda ta tsaya ta ce “To ki je ki kama ki yi zaman kan naki mana, ke dama banda Abba a tsaye yake a kanki, ai ƴar zaman kantan za ayi, kuma ƴar gagara”.
Nabila ta buɗe baki za ta yi magana, suka ji gyaran muryar Abba, daga saman bene. Tuni idon Nabila yayi jawur, saboda kuka da ɓacin rai.
Ya ce “Magajiya” cikin sauri ta ce “Na’am ranka ya daɗe”
“A gabanki kina tsaye yaran nan suke faɗa? Ki ka kasa tsawatar musu?”
Ta risuna ta ce “Tuba nake ayi mini afuwa”.
Sauda ta ce “Wallahi Ab….” Ya dakatar da ita ya ce “Ban tambaye ki ba, kukan me ki ke yi ke kuma?” Yayi maganar yana kallon Nabila.
“Faten wake aka yi, ba a dafa mini komai ba, kuma yunwa nake ji”
Ya ce “Wannan abun kawai shi ne abun kuka kuma? Ke a rayuwarki ba zaki taɓa girma ba kenan?” Tayi shiru tana sheshsheƙar kuka, kukan da yake jin sa har zuciyarsa.
“Magajiya, ko aikin wa ki ke yi, ki ajiye ki sama mata abun da za ta ci, ba biyanki nake dan a farantawa wani a ɓatawa wani ba, duk ƴaƴana nawa ne, babu banbanci a tsakaninsu”
Ta risuna ta ce “In sha Allah Alhaji, za a kiyaye”
“Ke kuma, ki cigaba da faɗa da yayyenki, zaki ga yadda zan yi da ke. Kuma na gode da furunciki Arfa, zaki yi zaman kanki ko? Tun ina raye ki ke wannan iƙrarin, ranar da na mutu ban san me zaki aikata ba, kin kyauta” bai tsaya jiran me za ta ce ba, ya wuce ya koma ɗakinsa.
Sauda ta yi wa Nabila gwalo, Nabila ta ce “Ai ke yakamata na yi wa gwalo, ni na yi nasara, tun da an ce a ajiye aikin babarki ayi nawa, banza ƙatuwar kwabo” Nabila ta wuce ɗakin su, tana tunanin ko dan wannan tijarar, ya isa tayi fatan tayi aure ta bar gidan nan.
***
Ɗan siririn matashi ne dogo, wankan tarwaɗa, sanye da kakin ƴan sanda, da ɗan hanzari yake bin wata doguwar baranda, wadda ta sa da shi da wata ƙofa.
Ya buɗe ya shiga da sallama, ya sarawa wanda ya tarar a cikin ofishin, wanda da gani babu tambaya, ka san babba ne sosai a cikin rundunar jami’an tsaro, duba da yanayin ranks ɗin da ke maƙale a kafaɗar uniform ɗin sa, da kuma haɗuwa da tsaruwar office ɗin na sa.
Ya ƙame tare da sarawa mai office ɗin, ya yi masa alama da ya zauna.
Ya zauna tare da sake gaida wanda ya tarar a office ɗin, da uniform ɗin sa ke ɗauke da sunan ACP Solomon wada.
ACP wada ya kalli matashin ya yi murmushi ya ce “CSP Nasir Yusuf”
Nasir ya waro ido ya ce “Wane ni Yallaɓai, Dsp ɗin dai”
“Au Csp ɗin ne ba ka so? Ba abun mamaki ba ne ba, ka ji gobe kai ne Cp na garin nan, kai koma IG gaba ɗaya”
Nasir yayi murmushi yana sunkuyar da kai.
“Ƙwazon mutum babu in da ba ya kai shi, kuma kar ka yi mamakin ƙwazonka ya kai ka in da ba ka zata ba. Yanzu ba karatunka da kuma ƙwazon ne ya kawo ka matakin da ka ke yanzu ba?”
Ya jinjina kai ya ce “Haka ne ranka ya daɗe”.
Acp Wada ya ce “Good, wani aikin za’a sake baka, wanda mu ke buƙatar sa da gaggawa, direct order ce daga Cp,ya kuma ce a jinjina maka aikin office ɗin ka yana kyau”
Nasir ya tattara hankalinsa ya ce “Ok sir, na gode sosai”
Solomon wada ya ce “Nasir, idan ka mayar da hankali yadda ake so, ka gudanar da aikin nan, za ka samu cigaba a aiki sosai da sosai”
Cikin girmamawa ya sake cewa “I will do my best in sha Allah”.
“Good” ya ɗaukko wani file ya ajiye masa, sannan ya ce “Kwanakin baya, akwai wani ɗan daba, da ya addabi garin nan, kai ɗan garin nan ne za ka fi ni sani, wai shi Aminu ana yi masa laƙabi da viper.
Shekarun da suka gabata yana tsare, sakamakon laifin da ya aikata, kafin kwatsam mu samu sanarwar cewa an sake shi. So bayan sakin nasa, akwai kokwanto a cikin sakin da aka yi masa ba bisa ƙa’ida ba ne ba, duk da controllern gidan yari ya ce order aka bashi ya sake shi, bayan fitowarsa ya cigaba da aikata miyagun laifuka a ɓoye, na sayar da miyagun ƙwayoyi tare da ƙyanƙysar sabbin ƴan daba, da suka hana jama’a zaman lafiya a garin nan, wanda yaƙi da wannan a ƙarƙashin kulawar office ɗin ka yake, a zone ɗin. Abun da muke so da kai shi ne, Aminu ya shigo hannu, ko ta halin ƙaƙa.”
Nasir ya ɗan yi shiru sannan ya ce “Ok sir, tabbas cases na dillancin ƙwayoyi da harkar daba, yana ƙara ta’azzara, amma laifin me yayi aka kai shi kurkuku? Kuma ya aka yi, aka sake shi ba bisa ƙa’ida ba?”
“Wannan ba huruminka bane ba, duk ba shi ne a gabanmu ba, kamo yaron shi ne abun da muka saka a gaba, wannan abun da ya shafi shari’a ne, ɓarnar da yake aikatawa ta yi yawa. Kuma a zone ɗin ka yaransa suka fi yawa, dan haka ka je ka yi iya ƙoƙarin ka a kai. Yabawa da nustuwarka, da jajircewar ka ya sanya muka baka aikin nan, ina nan ina saurarenka, ba a buƙatar ɓata lokaci. Ka je ka duba file ɗin a tsanake, akwai sauran informations da za su taimaka maka wurin kama yaron, da duk wani record na criminal acts ɗin sa yana ciki. Nan da gobe in Allah ya kaimu zaka dawo mini da file ɗin. ba na buƙatar kuma ka yi wani abu sama da haka, kar ka ƙetare iyakar da na gindaya maka”.
“Ok sir, i will do mai best in sha Allah” ya ɗauki file ɗin, tare da sake sara masa ya fita.
Ɓangaren Nabila kuwa, al’amuranta ba a samu sauyi ba, dan duk shari’ar da ba ta yi mata ba, ba za ta mayar da hankali a kai ba.
Director kuma ya bar ta ne, saboda mutuncin mahaifinta Major Yusuf da yake gani, mutum ne na gari kuma akwai tarin alkhairai da ya yi masa, shiyasa ya ƙyale Nabilatake cin karenta babu babbaka.
Nabila gaba ɗaya wasu lokutan sai ta ji tana danasanin karantar ɓangaren shari’a, yadda wasu abubuwan suke gudanawa sam ba sa yi mata daɗi.
Hausawa suka ce sai hali ya zo ɗaya ake abota, ɓangaren ƙawarta sumayya ma haka, kusan ƙalubale ɗaya suke fuskanta, dan har gara ma Nabila tana da alfarma a wurin na ta aikin, Sumayya kuwa na ta babu sani babu sabo.
Yau ganin motar Abba a gida bayan ta dawo daga aiki, ya sanya ta fuskanci yana gidan, dan haka da ta zuba abincinta, sai ta hau saman benensa.
A falonsa ta tarar da shi da Yaya Nasir, suna magana, da alama magana ce mai muhimmanci suke yi, sai dai yayi shirin fita.
“Abba sannu da gida” “Yauwwa” ya amsa a taƙaice.
Sai dai ta na zama ya tashi ya yi wa Nasir sallama, ya fita ya bar falon.
Nasir ya galla mata harara.
A shagwaɓe ta ce “Dsp me na yi ne? Kwana biyu duk Abba ya canza mini, kai ma kuma kana hararata”
“Ba dole ya canza miki ba, duk kin gallabi kowa a gida, bayan na dawo daga kaduna ake gaya mini wai kin je biki kin yi dare, ƙarshe a haraba ki ka kwana yayi punishing ɗin ki, ba ki zo kin bashi haƙuri ba. Law firm ɗin ku director ya kawo masa ƙara, daga danna waya sai kwalliya ki ka iya, ba kya son aiki, yayi ta bashi haƙuri ya ce a kula da ke a koya miki aiki, ko ba a biya ki ba, shi zai din ga biyanki salaryn. Kwatsam jin kunnensa ya ji ki na cewa ba dan shi ba, zaman kanki zaki yi, kin san kwana nawa ya ɗauka ba ya bacci saboda wannan maganar da ki ka yi? Duk cikinmu babu wanda Abba yake lelensa kamar ke, amma sai ba shi kunya ki ke ko ta ina?”
Cikin sanyin jiki, da tashin hankali ta ce “Innalillahi wa Innalillahi raji’un, ban zaci ran Abba zai ɓaci har haka ba, to kuma ba ka bashi haƙuri a madadina ba? Yaya sauda ce fa take ce mini agola, ni kuma ba na son na gaya masa. Ba na son fushin Abba, dan Allah ka tayani ba shi haƙuri. Maganganun Sauda ne suka ɓata mini rai, na yi dana sanin abun da na faɗa, amma dan Allah Yaya Nasir ka bashi haƙuri”
Ya girgiza kai ya ce “No ni ba ruwana”
Kuka ta saka masa tana cewa “Wallahi ba zan ci abinci ba, sai yanzu na ji maganar da na yi, ta yi nauyi ban san abba zai ji ba”
“Kin ga ya isa, kar ki saka ciwonki ya tashi na shiga uku, ya mayar da fushin da yake yi da ke kaina” ai kamar ya sake tinzirata, ta cigaba da sheshsheƙar kuka.
Cikin tsawa ya ce “Ke wai dan ubanki meye haka? Am i your mate, ba magana nake yi miki ba?” Sai da ta razana, amma hakan bai saka ta daina kukan ba.
Ya zuba mata ido, Nabila tun asalinta tun tana yarinya take fama da taurin kai na tsiya, yanzu ko dukanta zai yi, ba za ta daina kukan da take yi ba, balle ma yanzu ba wannan dan ta girmi duka. Har mamakinta yake yi, ƙatuwar budurwa ta kammala degree, kusan shekara ashirin da huɗu amma tana abu kamar yarinya ƙarama. Tsaki yayi, ya tashi shi ma ya fice, ya ƙyale ta, ta ci uban kukanta, ta kwanta a kusa da flask ɗin Abincinta ta hau baccin gajiya.
A tsanake Nasir yake duba file ɗin da aka bashi, a kan Aminu viper, da aka ce lallai ya kamo.
A record ɗin da ya duba, ya gano zuwan Aminun gidan yari, ba sau ɗaya bane ba, a kan mabanbanta laifuffuka da suke da alaƙa da harkar daba, da ta’amalli da miyagun ƙwayoyi.
Sai dai abun da ya ɗaure masa kai, ba a shigar da dalilin da ya sanya, aka kai shi prison na ƙarshe ba, an dai nuna ya aikata wani babban laifi ne, da ga cikin manyan laifuka da bai kamata daga lokacin faruwar abun zuwa yanzu ace an sake shi ba, haka zalika an cire wasu abubuwa masu muhimmanci da yakamata ace ya gani a cikin file ɗin, sannan ga shi solomon Wada ya yi masa umarni da ya yi amfani da iya abun da aka bashi.
“To menene dalilin haka?” Ya tambayi kansa, a lokacin da kan na sa ya ƙara ɗaurewa.
Sake duba file ɗin yayi yana tunani, kamar ya taɓa duba wani case, makamancin record ɗin da yake cikin file ɗin, sai dai kamar sunan ba haka yake ba.
“Aminu Viper” ya sake maimaitawa.
Ayshercool.
08081012143
[8/29, 8:34 PM] Halimatu A/Rahman Sadeeya: ⚔️*ƘARFE A WUTA ⚔️
AISHA ADAM AYSHERCOOL
3
Sama-sama Nabila ta ke jin hayaniya a kanta. Amma ta ƙi motsawa.
“Ke Arfa” yayi maganar yana riƙe hannunta.
Tashi ta yi zaune tana buɗe idonta a kan Abba, a sanyaye ta ce “Abba ka dawo?”
“Na dawo, tun da na tafi ki ke kwance a nan, ko abincin ba ki ci ba?”
“Abba Yaya ne ya ce kana fushi da ni, dan Allah ka yi haƙuri ba zan sake ba”
Major ya ce “Eh ya kira ni ya gaya mini, na haƙura tashi ki wanke fusarki ki zo ki ci abincinki” ta tashi ta shiga banɗakin falon, ta wanke fuskarta, ta zo ta zauna ta saka spoon ta fara cin abincin.
Ya numfasa ya ce “Rashin ji ne, ya yi miki yawa arfa, duk yadda na so na yi haƙuri sai kin ƙure ni, ban bi daɗin abun da kunnuwana suka jiye mini ba, kina iƙrarin zaki yi zaman kanki”
“Abba ka ce fa ka haƙura, ba zan sake ba”
“To shikenan na ji, ci abincin”
Umma tayi sallama da flask ɗin shayi, matarsa ta biyu, kasancewar yau girkinta ne.
Ta zauna a kusa da shi, ta haɗa masa tea, ya karɓa yana sha ya na yi wa Nabila hira, kamar bai yi fushi da ita ba, har ta ɗan ware.
Kiran sallar magariba ne, ya sanya ta tashi ta bar ɗakin, dan umma ta ji haushin zaman da Nabila ta yi, ita kanta Nabila ta so ba su wuri, amma Abba ya cigaba da jan ta da hira.
Da ya dawo daga sallar magariba, kai tsaye ɓangaren mama ya wuce, tana zaune a falonta, da Sauda su na kallon tv.
Gyaran murya yayi, sannan yayi sallama, suka amsa suna yi masa sannu da zuwa.
Ba tare da ya amsa ba ya kalli Sauda ya ce “Sauda nan gidan waye?” Ta ɗan yi turus tana kallonsa.
“Ki amsa mini”
“Gidanka ne Abba”
Ya ce “Masha Allah, idan ba zaki iya zama da ni, da tsarina ba, ko ki koma gidan tsohon mijinki, ko kuma ki fitar da miji ki yi wani auren”
Cikin damuwa Mama ta ce “Major me yayi zafi haka?”
“Baƙar aƙidar ki, da ta ara ta yafa, ba zan lamunta ba. Kun sani ba na ɗaukar duk wani abu da ya shafi Nabila da sauƙi, yadda na yi mata shamaki, da wanda ya zama katangar rayuwarta, dole na tsaya tsayin daka, na kula da ita kamar yadda na yi alƙawari. Ba zan lamunci a cigaba da wulaƙanta mini ƴa ba, har ta fara iƙirarin za ta yi zaman kanta. Babu wani ɗa da ya fi Nabila a cikin gidan nan, idan ki ka sake ce mata agola, to zaki fita ki bar mini gida ki nemi wani uban”.
Cikin takaici mama ta a ce “Amma da kunnenka ka ji ta faɗa mata haka? Ka san dai makirci irin na yarinyar nan ko?”.
“Kunnena ne ya jiye mini, ko zan yi mata ƙarya ne?”
Suka yi tsur-tsur baki daya.
Ya ja guntun tsaki ya bar falon.
Yana fita sauda ta ce “Mama dan Allah sai yaushe Abba zai daina fifita yarinyar nan a kanmu, tun da aurena ya mutu bai taɓa yi mini gori ba sai yau, saboda ita?”
“Ba ke kaɗai ba, ni kaina yadda ki ka san na yi mata kucciya, duk ita ce matsalar gidan nan, amma zan kawo ƙarshen komai da kaina, ki bar ni da su”.
Nabila kuwa na ɗakinta, itakaɗai, tana duba document ɗin shari’ar da director ya saka aka ba ta, sai dai gaba ɗaya ba ta da intrest a kan shari’ar, da ta gaji ma, ajiyewa ta yi ta hau waya da saurayi.
Wata matashiyar budurwa ce ta shigo ɗakin ta ce “Wallahi Nabila abun da ki ke yi ba kya kyautawa”
Nabila ta ɗan kalli Asiya, ta katse wayar ta ce “Da na yi me?”.
“Kin saka Abba ya yi wa mama da Anty sauda kaca-kaca saboda ke, sai da Anty sauda ta yi kuka”.
“To ai cewa zaki yi, Abba bai kyauta ba ni meye nawa a ciki?”
“Amma ke ki ka gaya masa ta ce miki Agola, bayan yayi musu mu ma ya iskemu a babban falo, ya yi ta yi mana faɗa”.
Nabila ta ce “Ashsha, ai kin san ni bana kai ƙara, ko dai na ɗauki mataki, ko kuma Allah ya saka mini da gaggawa”
Asiya ta ce “Ai shikenan, kowa yayi na gari kansa”.
Nabila ta ce “Allah ya yaye miki Aisya, ke ma fa matar nan idan ta tashi karta miki wulaƙanci, ba saurara miki take yi ba, daga ke har umman, amma ku yi ta bin ta kamar wata shugaba, ni dai ba mai takani ban ɗaga ƙafar na karya ba”
“A’a ai ke ki ka ce, ke ki na da ma dogara”
Nabila ta yi tsaki, tare da furta “Allah ka aurar da ni na huta da wannan kacaniyar gidan, Ya Allah dogo mai gemu” ta fita daga ɗakin tana addu’a.
Bayan kwanaki takwas.
A tsaye yake ƙyam, kamar ƙofa, kasancewar in da yake a tsayen ba a iya ganinsa sosai saboda duhu, sai dai inuwarsa ta nuna dogon mutum, kakkaura.
Ya ɗauki ɗankwali, ya ɗaure kansa da shi, tare da naɗo ɗankwalin ya rufe fuskarsa sai idanunsa kawai ya bari a waje.
Ya laluba hannunsa, ya ɗaukko wata irin doguwar wuƙa, ɓangare ɗaya zarto, ɗaya kuma kaifi, ga ta da uban tsini, a ƙalla za ta yi kamu uku, ya ɗaga rigarsa ya soketa.
Ya sake ɗaukar wata ya soke a jikin wandonsa.
Yanayin takun da yake kawai, ya isa ya tabbatar daƙaƙarfa ne, saboda yadda ƙasa ke amsa takun nasa.
Bayan wasu awanni, duhun dare ya ƙara yi, sahu ya ɗauke, sai haushin karnuka ko ina.
A ƙofar wani gida ya tsaya, ya din ga waige-waige, ya tabattar da babu kowa. Tamkar ɗan biri, haka ya cafke katangar gidan ya dira ciki.
Ya saka mukulli, ya buɗe wata ƙofa a cikin gidan da duk ta yi ƙura, ya buɗe ta ya kutsa kai ya shiga ciki.
Tsayawa yayi ya kunna fitilar wayarsa, yana haske ɗakin, take ya ji wani abu mai tsananin ɗaci ya fara kaiwa da komowa a ƙirjinsa, ya ji numfashin sa na barazanar barin ƙirjinsa.
Jikinsa ne ya fara rawa, ya ji tamkar hankalinsa zai gushe, ya durƙusa a wurin yana wani irin haki, cike da wani yanayi na mai shirin fita hayyaci.
Hayaniya ya fara jiyowa a waje, hakan ya saka shi miƙewa tsaye babu shiri.
Cikin sauri ya fito daga ɗakin, ya kama katanga, ya leƙa, sai dai yana leƙawa ya ga ƴan ƙato da gora da miyagun makamai, sun fara taruwa a kewayen gidan, kasancewar akwai hasken farin wata, kuma akwai hasken ƙwayayen solar hakan ya bashi damar ganin makaman da suke hannun su.
Babu tsoron komai, ya haye katangar, ya hau saman roofing gidan, ya dira ta wani ɓangaren, jin sautin dirarsa, ya sanya suka rufa masa baya, ta in da suke jiyo sautin gudunsa har da karnuka su na kururuwar a tare.
Sai dai duk da wannan ƙira da Allah ya yi masa, ta siffar ƙarfi ba ya jin nauyin jikinsa, ya din ga dukan ƙasar da dukkanin nauyin jikinsa, ba su ankara ba, ya ɓace musu ɓat kamar walƙiya.
A bakin titi suka tsaitsaya suna haki, su na mayar da yadda aka yi.
Ɗaya daga cikin su ya ce “Anya yaron nan, ba da layar zana yake amfani ba?”
“Ba wata layar zana, tsohon hatsabibi ne kawai, ni na yi mamaki ma da ya gudu ai, da da ne fa, wallahi sai ya illata ku kan ya gudun. Ai kamar yadda na gaya muku ne, da na ji alamun ya zo, zan kira ku a waya na sanar muku, ai ba zan sake sukuni ba sai ya je hannu, na za ta ma zaku kira ƴan sanda ne”
Ɗaya daga cikin jami’an sintirin, ya ce “Ko zamu kira ƴan sanda, mu yakamata mu fara huɓɓasa mu kama shi, sai mu miƙa musu shi, wannan gudun nasa yaushe muka kira ƴan sanda ma”
“Amma duk da haka, yakamata su san yana zuwa ai”
Shugaban su ya ce”Muddin suka sani, canza taku zai yi, ba zai sake zuwa ba”.
Malam lawan da gidan sa ne a jikin gidan da yake zuwa ya ce “In ji wa? Ba zai taɓa iya daina zuwa gidan nan ba, yadda ka san ya binne asiri a ciki, kodayeke sai ta yiwu ma asirin ya binne, wannan hatsabibancin nasa akwai lamarin sihiri a ciki, amma zan cigaba da saka ido, da ya zo zan kuma kiranku”
“To shikenan malam lawan mun gode, yanzu ka koma gida, bari mu koma bakin aiki, ko kuma a raka ka ne?”
“Ahha haba, kamar ba namiji ba, ba wani abu bari na koma, ai ya riga ya gudu” Suka yi sallama ya nufi layinsu.
Sai dai yana daf da ƙarasawa gidansa, kawai ya ji an yi ball da shi, kasancewar sa ɗan ƙaramin mutum, sai jin sa yayi, ya yi sama ya dawo ƙasa kamar wani karmami. Ya tashi a gigice yana zaton ko gamo yayi da aljani, ya hau waige-waige.
Haske shi ya yi da fitila, sannan ya ce “Kwana da yawa malam lawan, tsohon butulu, da na ƙyale ka ban yi maka komai ba, shi ne ka cigaba da yi mini bita da ƙulli?”
Cikin kwakwazo, da tsananin razani ya ce “Na tuba, na bi Allah na kuma bi ka, dan Allah” kan ya ƙarasa, ya karya shi ɓaras, ta hanyar saka ƙafa, ya yi masa wani irin duka a ƙafarsa ɗaya.
Malam lawan ya a kurma ihu, cikin tsananin zafin nama, ya cire hular kan malam lawan,, ya tura masa a baki, sannan ya ciro wuƙar ƙugunsa ya yanke shi a damtsensa, aikuwa jini ya ɓalle.
Ya durƙusa a gaban sa ya ce “Yanzu ai ka ji daɗin bayar da rahoton zuwana, ragon maza kawai” ya tashi tsaye ya ja da baya ya ɓace a cikin duhu, ya bar shi a mawuyacin hali, ga karaya ga yanka, gashi kuma ya toshe masa baki.
Ko da ya koma gidansa da yake zaune, ciro wuƙar da ya yanki malam lawan yayi, yayi jifa da ita. Ya tsaya yana haki, abun da ya yi alƙawarin dainawa, yau ya yi, ya zubarwa da wani jini.
Ya dafe kansa yana huci cikin tsananin damuwa.
**
Yau sumayya ba ta haɗa tafiya da Nabila ba, dan da wuri sosai ta fita, za ta shiga asibitin murtala ta duba wata yayar babansu da aka kwantar a emergency, za ta kai musu abinci.
Su na tafe da mai adaidaita sahu, ta hango mutane na ta shiga su na fita a wani layi, duk da lokacin gari bai gama hasken da za ace, mutane suna wannan tururuwar ba.
Da sauri ta tsayar da mai baburin, ta biya shi kuɗinsa, ta sauka, ta nufi layin da mutane ke shiga su na fita.
Wurin duk babu mata, sai maza, amma hakan bai hanata kutsawa da son gano abun da yake faruwa ba.
Tsayawa ta yi ta tambayi wani magidanci, abun da yake faruwa. Ya sanar da ita, gawar wani yaro aka tsinta, a bayan maƙabartar unguwar, an yanke masa al’aura da wasu sassa na jikinsa.
Jikinta na tsuma ta cigaba da kutsawa tana faɗin “Ku matsa, ni ƴar jarida ce” tare da nuna musu id card ɗin ta.
Ta ɗaɗɗauki hotunan yaron, sannan ta tsaya tattaunawa da mutanen da suka fara zuwa su ka tarar da abun.
Sai kiranta ake yi a waya, ana jiran ta kai abinci, amma sai da rana ta ɗaga sosai, aka gama komai ƴan sanda suka zo, sannan ta yi shirin tafiya, shi ma sai da ta karɓi lambar wayar wani ɗan sanda, da zimmar zai din ga ba ta update na sakamakon binciken da za su yi, a kan gawar.
Ko da ta je asibiti ta sha faɗa,na rashin kai musu abinci da wuri, ko a jikinta, saboda ta samu rahoto, dan haka tana ajiye musu abincin, ta yi waje.
Sai dai ba ta fito daga emergency ba, ta din ga jin ihun wani babban mutum, kamar mara gaskiya, haka ta koma tana leƙawa ta ga abun da yake faruwa.
Magidanci ne, ake yi masa ɗinkin wani uban yanka a damtsensa, jikinsa yayi kaca-kaca da jini, duk da ana ta yi masa allaurar kashe zafi, amma sai ihu yake yi.
Babu neman izni, ta afka ciki ta ce “Sannu bawan Allah, ka yi haƙuri Allah ya baka lafiya, ka daure”
Duk sauka waiwayo su na kallonta, har da ma’aikatan, mutumin ya ce “Na gode sosai”
Ta ƙara matsawa ta ce “Amma hatsari ka yi ne? Kodayeke wannan ai yankan makami ne ba hatsari ba”
Ya ce “A’a wani ɗan daba ne, ya sare ni jiya cikin dare, dama hukuma ta daɗe ta na neman sa”
Sumayya ta gyara tsayuwarta ta ce “Subhanallah, bawan Allah a wace unguwa ce haka? Ko rigima ku ka yi da shi ne?” Ƙanin malam lawan da yake tsaye a wurin, a fusace ya kalli sumayya ya ce “Dalla malama fita, mutum yana fama da kansa, kin zo ki na yi masa wasu surutan banza”
Ta ce “A’a Allah ya baka haƙuri, ka sani ko akwai wani taimako da zan iya yi masa. Kalli saran da aka yi masa fa, idan ba za ka damu ba, zan naɗi muryarka, mu saka a radio, ko Allah zai saka, hukuma su bi maka haƙƙinka, barin su da ake yi suna cin bulus ya sanya suke cigaba da ɓarna”.
Malam lawan ya ce “Ke rufawa kanki asiri, hatsabibanci da ta’addanci yaron, ya wuce tunanin ki”
Sumayya ta zaro wayarta, za ta yi magana, sai ga wasu mutane guda biyu sun shigo da wani kaki a jikinsu, da ba ta san na menene ba, suka mayar da ƙofar ɗakin suka rufe.
Malam lawan ya kalle su, ba su ne ƴan sandan da aka kirawo suka tsaya masa, likitoci suka zo kansa ba ne.
Sumayya ta yi tsilli-tsilli da ido, ɗaya ya ƙirga mutanen da suke cikin ɗakin, da likita ɗaya, nurse ɗaya, sai ƙanin malam lawan da sumayya. Dan duk maƙwabtan da suka kawo shi, sun tafi wurin sana’oin su. ya ce “Ku biyar ne a ɗakin nan, idan ka sake mu ka ji labarin sunan wanda ya yi maka wannan raunin, to za ka maye gurbinsa da ya bari na gidan yari, dan haka ka ja bakinka ka yi shiru”.
Sumayya ta ce”Ban gane ba Yallaɓai, mutum mai laifi kuma ace kar a faɗi waye? Ba ka ga irin illar da aka yi masa ba ne, ga karaya ga rauni, da ya kashe shi fa?”
Ya ba ta amsa da “Da ya kashe shi, bakinki zai iya sakawa, ki ɗauki hukuncin da za ayi masa na kisan” daga nan suka juya suka fice.
Mamaki ya mamaye sumayya, ta ce “Kai kuwa bawan Allah, waye wannan shi kuwa, da har jami’an tsaro masu kaki, za su hana bayyana laifinsa, ana sane aka ƙi kama shi kenan?”
Malam lawan ya ce “Ba zaki ja mini masifa ba, ki fita ki bar wurin nan, na ji da masifa ɗaya, bayan ɗinkin nan a karye nake wallahi”
Cikin tsananin naci, da son samun rahoto, ta kwantar da murya za ta lallaɓa shi, ta samu labari, amma da likitan da ƙaninsa suka koreta daga ɗakin.
Fitowa ta yi, tana ta mamakin abun da ya faru, yaya za ayi hukuma ta bawa mai laifi kariya, wane irin abu ne haka?.
Ba ƙaramar makara ta yi ba, amma tunanin abun da ya faru, ya fi ɗaure mata kai.
***
Sannu a hankali yake yi wa kansa allura, yana yi yana fatan samun abun da yake so, a hankali ya gama ɗurawa jijiyarsa ruwan allurar da yake fari tas a cikin sirinji, bayan ya kammala tsaf ya fara jin kansa yana yi masa nauyi.
Take idanunsa suka yi mitsi-mitsi, ya soma lanƙwasa kansa, yana jin idanunsa kamar za su fito waje, suna yi masa yaji, a haka ya kunna sigari, ya kashingiɗa, ya na bawa sama hayaƙi,yana jin yadda jikinsa ke son bijirewa aikin allurar.
Wayarsa ce ta fara vibrating, ya miƙa hannu, ya ɗaukkota ya duba, yana zaton ko a cikin yaransa ne, sai dai ya ga private number ce.
Har zai ƙi ɗagawa, sai kuma ya ɗaga ya saka a kunnensa, amma bai yi magana ba.
Daga cikin wayar aka ce, “Meyasa ba ka gajiya da neman magana ne? A wannan karon ma sai da ka saka na yi abun da na goge ɓarnar da ka yi, yakamata ka nutsu Aminu”
Ya saki hayaƙi, tare da ɗan kaɗe tokar da sigarin ta tara, sannan ya ce “Waye kai? Sannan waye ya saka?”
Mutumin yayi dariya, ya ce “Mutum mai ba ka kariya, domin cimma nasa muradin, yakamata ka sauƙaƙa mini aiki, ka daina aikata abubuwan da za su din ga barin trace a kan ka”.
“Ka yi muguwar kasadar ƙoƙarin cimma burinka da mutum irina, kar ka manta viper ake yi mini laƙabi da shi, macijin da ya fi kowanne hatsari, idan ka bari na sare ka, ka gama yawo” yana gama maganar ya cillar da wayar, ya ɓata fusaka kamar ya fashe da kuka.
Cikin fusata ya ce “Ni again? wani ya kuma amfani da ni? Impossible zan watsa dafina a in da ya dace da in da bai dace ba, sai na tabattar da danganawa ga kunyar ƙarshe, ko da kuwa za ayi mutuwar kasko” ya yinƙura da nufin ya tashi tsaye, amma ya kasa sarrafa gangar jikinsa, hakan ya tilasta masa komawa ya nemi wuri ya kwanta.
Duk da irin faɗan da sumayya ta sha a wurin aiki a kan makara, bai dame ta ba, jikinta sai tsuma yake saboda ta zo da rahotanni masu muhimmanci da ɗaukar da hankali.
Ofishin head of news ta je, ta shiga da sallama.
Matar ta ɗago ta amsa mata da ƙyar, ta ƙarewa sumayya kallo, ta ce “Yanzu ne lokacin shigowa aiki ko? Gaba ɗaya yaran yanzu ba kwa ɗaukar aiki da muhimmanci, kodayeke karatun ma ba wani na kirki ku ka yi ba, duk da satar amsa ku ke gamawa. Ki shiga hankalinki kafin na kai maganar nan wurin MD”
Sumayya ta risuna ta ce “Afuwan anty, in sha Allah ba zan sake ba, na samu wasu rahotanni ne masu muhimmanci, da ya san na tsaya a hanya, shiyasa na makara na kawo miki a tantance ne ko za a saka su a news”
A yamutse matar ta ce “Na menene” cikin farinciki da jin ƙwarin gwiwar ta yi abun arziki ta fara da gaya mata abun da ya faru a asibiti.
Amma matar sai cewa ta yi”Amma ba ki da hankali ko? Ta yaya zamu saka wannan shirmen a news?”
“Anty ai a rahotanni, ko a janyo hankalin hukuma…. “Dalla yi mini shiru, business mu ke yi a nan mu, ke fa iyayinki da rawar kanki yayi miki yawa sumayya. Meye hujjarmu idan aka tsutsiye mu, cewar hukuma na ɓoye mai laifi?”
Sumayya ta ce “Wallahi a gabana aka yi, mutumin yana nan a emergency”
“Kin ga idan ba ki da abun faɗa, fita ina da abun yi”
Sumayya ta yi iya ƙoƙarin ta, ta danne abun da yake taso mata na fushi ta ce “To shikenan, sai kuma akwai abun da na gani, ina kan hanyar tahowa nan, a nan wajen gari, an tsinci gawar yaro an cire masa wasu sassan jikinsa”.
“Almara kenan, wa zai yadda da wannan zancen?”
“Ba zance ba ne ba, na yi recoding ɗin maganar wasu daga mutanen da suka fara cin karo da abun”.
“Sumayya, ba irin wannan labaran mu ke buƙata ba dan Allah, je ki su murtala sun fita neman rahotanni, ki din ga kawo sensitive abubuwa”
Summaya ji tayi wata irin ashar na kai komo a wuyanta, da take ƙoƙarin narkawa matar nan, ta rasa abun da ta yi mata, haka kurum ta tsane ta. Ta yi ta kyararta ba ta son ta ga tayi wani abu na cigaba.
Sumayya ta fice daga office ɗin kamar ta yi kuka, ta koma reception ta nemi wuri ta zauna.
Ba uwar da ta tsinana a aikin yau, tun da head of news department ta yi mata wulaƙanci.
Kasancewar a makare ta je, ya sanya lokaci yayi gudu, Lawisa, wato head of news ɗin, ta din ga shiga tana fita, ta na kaiwa tana komowa, idan ta kalli in da Sumayya take sai ta haɗe rai.
Wannan karon bayan ta fita, a tare suka shigo da managern director, sai karairaya take yi masa, tun da ya shigo ma’aikatan suke ta gaishe shi.
Ban da sumayya da ɓacin rai ya saka ta cika ta batse.
Sai da yayi gyaran murya ya ce “Wannan ba sabuwar staff ɗin mu ba ce? Ya na ganki a nan? Wane department aka kai ta ne?”
Lawisa ta yi caraf ta ce “Sir ba ta da ƙwarewar aiki ne haryanzu, ana ɗan nunnuna mata aiki ne, kafin ta gama gogewa”.
Ya ce “Ok, babu laifi” sumayya kamar ta kwaɗawa lawisa mari, a fusakarta da ta sha uban bleaching, duk tayi taruwar jini.
Ta daure ga gaida MD, sannan suka wuce gaba.
Tsaki Sumayya ta ja, tana duba wayarta.
Sai dai jin sallamar Nabila a reception ya sanya ta ɗago da sauri tare da amsa mata.
“Ya na ganki a nan?”
Nabila ta ce “Ke baki iya karrama baƙo ba ko?” Ta tsaya suka gaisa da admin ɗin da ke reception, sannan ta ƙarasa kusa da Sumayya ta zauna.
“Arfa, ya na ganki yanzu ne? Lokacin tashi daga aiki bai yi ba?”
“Kema ya na ganki a nan kamar mara galihu, ke baki da office ɗin da zaki zauna ne? Ki zo chambermu ki ga ofishin da aka bani hajiya, kamar wata sarauniya”
Sumayya ta ce “Eh ofishin da baki damu da aiki ba ko, sai sun dawo da ke gadin chamber tukuna”.
Nabila ta yi dariya ta ce “Kin san wani abu, wai nan aikena aka yi, zan je na lallaɓa na zo da wata mata, ko in tattauna da ita, sannan in je shagari firm, zan haɗu da wani lawyer, kuma ni wallahi kaina ciwo yake yi”
Sumayya ta kalleta ta ce “Ba zaki ba kenan?”
“Ai faɗa ma ɓata baki ne, sumayya wurin nan naku mai kyau, tashi ki rakani na zaga” duk da ran sumayya babu daɗi, amma ganin Nabila ya sanya ta jin sanyi a zuciyarta.
Suka shiga zazzagawa, ta kaita news room, sai dai su na buɗewa suka tarar da MD da lawisa a ciki, suna aiki.
Sumayya ta risuna ta ce “Am sorry sir, ban san ku na ciki ba, Arfa mu je ki ga….
“A’a tsaya mana na ga nan ɗin, Nabila ta shiga cikin fara’a ta ce “Yallaɓai ina wuni?”
Shima cikin fara’ar ya ce “Lafiya ƙalau, ya ki ke?”
“Lafiya lau sir, ina fatan ba zan takura muku ba, ina son sanin abubuwan da ban sani ba a rayuwata, mussaman wanda ba field ɗina ba, sister ina wuni?” Tayi maganar tana kallon lawisa da ta yi bala’in haɗe rai.
Lawisa ta takurawa Sumayya ne, saboda tana ganin ƴar gayu ce, ga ta baƙa amma baƙinta mai kyau ga ƙwazo, tana gudun ta ƙwace mata matsayin ta, kuma ita bazawara ce, a da a wurin babu wanda ya kaita gayu a wurin, amma yanzu sumayya ta fita.
Yanzu kuma ga Nabila, ita da take da hasken fata ma sosai.
Nabila ba ta san lawisa ta amsa ko ba ta amsa ba, ta ja kujera ta zauna, tana yi wa MD tambayoyi, a kan abubuwan da suke cikin news room ɗin.
Lawisa ta ƙulu,ta din ga harar Nabila, amma ko a jikinta, ita kanta sumayya sai da haushi ya kamata abun da Nabilan take yi.
Nabila ta ce “Yallaɓai, ko zaka saka mini lambarka, idan wani abu ya kama na aiki, zan iya taimakawa i am barrister Nabila Yusuf”
Ya ce “Wow, what a very young and beautiful barrister, kin zama lawyer da ƙananan shekaru, ya karɓi wayar Nabila, ya saka mata lambarsa, ta tashi ta yi musu sallama.
Sumayya kamar ta yi bindiga, su na fita ta din ga ɗurawa Nabila ashar, a kan abun da ta yi, tare da gaya mata alaƙar Lawisa da kuma MD.
Nabila ta ce “Sumayya, dan Allah kar ki ɓoye mini, idan yana da kuɗi na ci rabona, na ga zai yi son mata”
Ganin Nabila na neman mayar da ita mahaukaciya, sai ta canza maganar.
“Ke kin san menene? wai ni zan kai rahoto har kashi biyu, sakaryar matar nan ta ce ba za a saka ba, wai ba sa buƙatar irin wannan labarin, MD ya tambayi me nake yi a reception ba na aiki, wai ta ce masa ban iya aiki ba, na rasa uban da na tsare mata ta tsane ni, dama ni na samu damar da ake baki, a wurin aiki, in yi wata shida ina aiki a wurin, wai ban iya aiki ba, da yake kwanan nan ya dawo daga ƙaro karatu, tun da aka ɗaukemu ya tafi”.
Maimakon Nabila ta tausaya mata, sai ta hau dariya, “Ai kawai ki fara soyyaya da MD ko ta bala’i, shi ne zaki rama”.
Sai da ta ga Sumayya ta yi fushi sannan ta ce “Sorry my sumy, maganar gaskiya babu daɗi, kuma kishi take da ke kuma tana ƙoƙarin kare abun da take so, shikenan”
Idon sumayya ya tara hawaye ta ce “Sai kuma ta din ga daƙile ni a harkar aikina? Ta yi mini adalci kenan?”
Nan ta ba wa Nabila labarin abun da ya faru, daga fitowarta daga gida, zuwa yanzu.
Nabila ta ce “Na shiga uku, sumayya me ƙasarmu ke son zama ne? A zahiri an nunawa mutane ana neman mai laifi, a baɗini kuma hukuma na ɓoye shi? Duk yadda ake fama da ƴan daba da masu ƙwace a garin nan, tirƙashi ana maganin ƙaba kai yana daɗa kumbura, ke ba ki san sunan wanda ya yi laifin ba?”.
Sumayya ta girgiza kai ta ce “Ban sani ba, bai faɗa ba, korata ma suka yi”.
“Mu ƙarasa titi mu tari napep mu je asibitin, mu tattauna da shi mutumin, ni kin san ba na tsoron a mutu ko a yi rai. Sannan zan je na samu Yaya Nasir na yi masa maganar wannan ai abun kunya ne”
Sumayya ta girgiza kai ta ce “A’a, na tsorata da kashedin da aka yi mana, a bar zancen kawai, ban san suwaye mutanen ba”.
Nabila ta ce “Wallahi sai mun je, akwai wata shashasha da ta isa ta hana ki cigaba a rayuwa, idan ma ba a saka radiyo ba, sai mu kwatsa a media ina da mabiya sosai a social media, sai ayi duk wadda za ayi.!!!”
Ayshercool
08081012142
[8/29, 8:34 PM] Halimatu A/Rahman Sadeeya: ⚔️*ƘARFE A WUTA ⚔️
*AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
Page 4
“No Nabila, abun da ki ke yi is too risky, mutanen nan da gaske suke, they mean what they said, kar ki jefamu a matsala”
Nabila ta ce”Karatunki ya tashi a banza kenan sumayya? Idonki har da hawaye saboda takaici. Wasu lokutan kin fiye sokwanci sumayya, da ni ce da tuni na ci buhun ubanta”.
Sumayya ta ce “Ni ce sokuwa ko? na gode amma ni ba zan iya kasadar da ki ke yi ba, na rasa aikina, but wait mu je na rakaki in da aka aike ki mana”
Nabila ta ce “Wa? Taɓ tuni na kira MD na bashi uzuri, dama barrister Habib ne ya aike ni, yadda wannan matar ta wurin aikinku take, lawashi ko lotion take, haka yake yi mini, ba ya ƙaunata”
“A’a, naki ya sha banban da nawa Nabila, shi taimakonki yake yi ai”
Nabila ta kwaɓe fuska ta ce “Ke, idan fa kin ga ina zuƙewa a aikin nan, wanda za a kare ba shi da gaskiya ne, MD zan saka ya canza mini team daga na su Barrister Habib, na Barrister Bashir nake so, wata zazzafar shari’a za su kara, shari’ar manya ce, a kan kuɗi, zuwa zan yi na sha kallo, kuma an ce akwai yiwuwar na haɗu da masoyiyyata kwanan nan”
Sunayya ta ce “Wa kenan?”
“Anty Naja’atu Bunkure mana, kin san am die hard fan of that woman, Barrister Naja’atu duniya ce, ga gayu malam, harshenta akwai turanci, kamar wadda aka haifa royal palace ɗin Elizabeth”
Sumayya ta yi tsaki ta ce “Aikin banza ƴar wahala, ita ta zama abun da ta zama a harkar aiki, har tana burgeki, ke kuma kina zaune kina shashanci, wallahi ƙarshe ki koma ƴar ɗaukar jakarta”
Nabila ta ce “Kan uba, degree holder in yi dakon jaka, Kin ci mutuncina fa,
Sumayya ta girgiza kai, haryanzu Nabila shirirta da yarinta na damunta.
Ko da Nabila ta je gida, tun a tsakar falo take tambayar magajiya, ina DSP.
“Bai dawo daga aiki ba, na ji ɗazu yana cewa ko za su je ringin”
Nabila ta ce “Aikuwa ya yi ya dawo, sun bayar da maza, in mun zauna ya yi ta cewa police ya fi lawyer, yau zai sha kunya idan ya ji me suka yi. Yau zazzafan debate ne tsakanina da shi, har lemo zan yi mana aji daɗin yin musu”
Anty ta ce “Ka ji mashirirciya, musun da za ku yi za ki haɗawa lemo?”.
“Eh mana, ɗan sanda sharri, lawyer kuma musu” tayi maganar tana dariya.
Wani mugun kallo mama ta yi mata, yaran gidan nan har take suke yi wa Nasir da discipline master, saboda yadda suke jin tsoron sa, amma tsakaninsa da Nabila sam ba haka bane ba, suna good time sosai da Nasir, kuma duk gidan bayan Abba ba ta da abokin hira ko shawara sai shi.
Nabila ta share mugun kallon da maman ke yi mata, ta tafi ɗaki.
Misalin ƙarfe huɗu na yamma, Sumayya ta ga kiran lawisa, kawai ta basar ta cigaba da kallon tv, ta kira ya kai sau huɗu sannan ta ɗaga.
“Ki na ji ina kiran waya ki ka ƙi ɗagawa?”
“A silent take, bacci nayi ne”.
“Ki tura mini recodings ɗin nan, su murtala ba su sami wani samo rahotanni masu muhimmanci ba, kuma na ga su Mikiya radiyo duk sun wallafa labarin yaron nan, ki turo mini mu ga wanda za a iya tacewa a saka” Sumayya ta taɓe baki ta ce “To”
Ta kashe wayar, ta ce “Allah ya ƙara, da mu muka fara sanar da labarin, kuma mu ka saka a internet, ai da ya fi, tun da ni ce ƴar jarida ta farko da ta fara zuwa wurin, amma ki ka ƙi”
Ta lalubo lambar Nabila ta kirata, ta gaya mata abun da ya faru. Nabila ta ce “Amma baki da wayo sumy, ke yanzu sai ki tura mata, saboda ba ki da zuciya?”
“To yaya zan yi mata?”
“To amma kin san ko kin tura mata, sunanta za ta faɗa a mai rahoton ko wanda ya karanta ba ke ba ko?”
Sumayya ta ɗan yi shiru ta ce “Kuma fa haka ne”
“To tun wuri ki ce mata kin goge kawai, gobe ba za ta ƙara yi miki wulaƙanci ba”.
Sunayya ta ce “Haka za ayi, na gode sosai” cikin hanzari ta kira Lawisa, ta sanar mata da cewa ba ta ga recordings ɗin ba.
Aikuwa ta hau ta da bala’i, Sumayya ta danna recording tana dariya ƙasa-ƙasa da niyyar ta turawa Nabila.
Bayan sun gama wayar, ta turawa Nabila, suka din ga dariya, Nabila na ƙara bata ƙwarin gwiwar, kar ta sake ta ɗauki raini ko wulaƙanci daga wurin lawisa.
Ta kuma cigaba da lallaɓa sumayya, a kan lallai ta koma asibiti, ta sake tattaunawa da mutumin nan, ko iya sunan mai laifin ta samo.
Barrister Habib ne ya shiga office ɗin MD, ya zauna suka gaisa, cikin takaici Habib ya fara magana, “Barrister, ni fa na gaji da iskanci yarinyar nan, idan a team ɗi na za ta zauna, ta zauna, kuma dole ta yi biyayya ga abun da na sakata, idan wurin Bashir za ta koma, ta koma na gaji da iskanci da rashin mutuncin da take aikatawa, ba ta san aiki ba ko kaɗan”
MD ya ce “Calm down Habib, na sani wallahi, na san ku na haƙuri da ita, wallahi nima nauyin mahaifinta nake ji ne, abun da yayi mini a rayuwa idan na kore ta ban yi wa kaina adalci ba, shi ma yana yawan bani haƙuri a kanta, marainiya ce kuma ba ta da cikakkiyar lafiya.”
“Mu ma duk marayun ne ai, waye yake iskancin da take yi? Ta zo lokacin da ta ga dama ta tafi lokacin da ta so, she’s not serious at all”
“Na sani, kuma nima ina gani, ka rabu da ita, duk wani abu da za ku yi ku daina sakata a ciki, ƙyaleta da bashir ɗin, shi ne daidai da ita, ku yi haƙuri dan Allah” MD ya din ga lallaɓa Habib, dan ba zai so rasa gogaggen lawyer kamar Habib a law firm ɗin sa ba, a kan Nabila da ba aikin ne a gabanta ba.
Yau weekends ne, gaba ɗaya iyalan major na babbn falo, kowa ya ja nasa wuri yana karyawa, Nabila ce kawai babu a wurin.
Tun yana jurewa ya kasa, yayi gyaran murya ya ce “Ina arfa ne?”
Anty ta ce “Bacci take yi”
Ya kalli walida ya ce “Tasota, ta fito ta karya, sai an cinye an bar ta, ta cikawa mutane kunne da kuka”
Kusan mintuna goma da taso ta, sannan ta fito, kayan bacci ne a jikinta, dogon wando da rigarsa har gwiwa, kanta babu ɗan kwali.
Nasir ya tsura mata ido, ko ƙiftawa ba ya yi.
Abba ya ce “Ina kallabinki? Ki ka fito da wannan gashin ba kyan gani, kamar totuwar masara?”
Ta saka hular hannunta ta ce “Haba Abba, dan daga bacci na tashi ne fa”
“Tafi can ƙazama, kullum kai babu kitso, ba za a rasa kwarkwata a wannan gashin ba” dariya aka hau yi mata.
Ko a jikinta, ta zauna kusa da Abba, ta kalli Nasir ta ce “DSP, yaushe ka dawo ba labari, ya hanya?”
Ya jinjina kai ya ce “Alhamdilillah”
Major da kansa, ya taya Nabila haɗa shayi, ga soyayyen dankali, ga bredin ta, amma tana buɗe bredin ta ce ba za ta ci ba, kwantai ne.
Major ya miƙa mata nasa ya ce “Duba zaki iya cin wannan? Dankali kawai ba zai riƙe miki ciki ba” ta duba buredin Abban ta ce “Eh wannan sabo ne, Abba ka ƙara mini ƙwan, ni ba na son dankalin ma”
Ya ce “To shikenan, ɗauki nawa da ma ni yanzu ƙwai bai dace da ni ba, a shekaruna”
Idan da sabo, sun saba da ganin irin wannan fifikon da major yake nunawa, duk da mutum ne mai ƙaunar yaransa sosai da sosai, amma son da yake yi wa Nabila na musamman ne, amma fa hakan ba ya hana idan suka yi laifi, ya hukunta su kamar ba ƴaƴan cikin sa ba.
Anty ta ce “Arfa ba zaki bari Major yayi ƙiba ba, kalli yadda ki ke tara mazaunai, saboda ci”
Yayi murmushi ya ce “Tafi kowa girma a gidan nan”
Nabila ta ce “Abba, Allah ya ƙara arziki, ka yi ta sayowa mu na ci”
“Amin arfan Abba”
Nasir ma ya juye mata nasa ƙwan, ta tattare tana dariya, dan ta na son ƙwai sosai.
Mama kuwa kamar za ta yi bindiga, saboda baƙin ciki.
Bayan an kammala cin abinci, su walida ne suka kwashe kwanukan da aka ci, Nabila kuma ta hau labartawa Nasir, abun da ya faru da sumayya da ta je Asibiti.
Fafur Nasir ya ce ƙarya take yi.
Ta haɗe rai ta ce “Yaya, wai meyasa a duniya jami’an tsaro ba kwa yadda kun yi laifi, ko wani ne daga cikinku yayi, sai kun ƙaryata, kun kare mutum”
“Wa ya gaya miki hukuma tana laifi?”
“Ba mutane ne hukunar ba? Ai mutane na laifi, kuma hukuma ma suna yi, wallahi da gaske nake, ka bincika ka ji kuma, koma na kira maka sumayyan”
Ya ce “A’a ai ƙarya ki ke yi, ni zaki zauna kawai dan ki ƙure”
Duk yadda ta so, ta fahimtar da shi, amma ya ƙi fafur.
Abba dai kallonsu kawai yake yi yana dariya, ganin ba zai yarda ba, ya sanya ta ƙyale shi, ta koma wurin Abba.
“Abbana” tayi maganar tana ɗan murmushi.
Abba ya ce “Kuɗi zaki tambaya kenan?”
Ta girgiza kai ta ce “A’a Abba, abu zan tambaye ka”
“Ina jin ki”
“Abba dama, wata amarya ce, suka kira ni a waya, zan je gida na yi musu make up, ita da ƙannenta na biki, za su biyani, VIP ne har gida”
Haɗe rai yayi sosai sannan ya ce “Me na gaya miki a kan wannan sheɗancin? Kin san na hana ki sabgar banzar nan, ban da kalen sheɗanu jikinku, me wannan shashancin zai amafana miki, na fuskanci kin fi fifita wannan kwalliyar a kan aikinki, to babu in da za ki je”.
“Dan Allah Abba, wallahi zan samu kuɗi fiye da salaryna, dan Allah”
“Ba in da zaki, tun da babu abun da ki ka rasa a gidan ubanki, ba matar da zaki bi gida ki na shafawa hoda, idan ta matsu tayi da kanta mana, banda shashanci ace mace ta zauna sai an bita gida shafa mata hoda da gazar”
“Abba!”
“Shut up” yayi mata tsawa, hakan ya tilasata mata yin shiru.
Walida kuwa faɗan Abban dariya ya bata, wai idan sun matsu su yi da kansu, ba wadda za aje gida shafawa hoda.
Nabila ta din ga jin ko a ɓoye sai ta je, tana son sana’arta ta kwalliya, Abba kuma ba ya so, wai shashanci ne da fatan aljanu, ita kanta idan tayi a fuskarta wasu lokutan, ya din ga faɗa kenan.
Akwai ranar da za ta je biki, ta yi kwalliya ta saka eyelashes, ya kirata dan ya ga meya samu idonta, gashin idonta yayi tsawo haka, tun da ta ce masa sawa tayi, ba ta ankara ba, ya saka hannu, ya fige shi sai da ya haɗa da gashin idonta, ya ce ya kuma ganinta da shi sai ya zaneta.
Har a gaban saurayi, ya taɓa korata gida, wai ta je ta wanke fuskarta, ba za ta cuci ɗan mutane ba, duk ta damalmala fuska da hauka, ta zama kamar wata bebin roba.
Ta rasa meyasa Abba yake adawa da sana’ar nan tata.
Nabila tun a weekend, take cigaba da zuzutawa Sumayya trial ɗin da za su je, kotu ranar laraba, farincikin ta ya kasa ɓoyuwa, wanda hakan ya samo asali ne, da yadda ta ga Barrister Habib ya ƙyale ta, ta koma team ɗin Bashir, kuma ta samu labarin barrister Naja’atu ma tana da shari’a ranar a kotun, dan haka za ta haɗu da ita.
Nabila uniform ɗin ta, tamkar su yi magana, saboda ɗaukar guga, ita kanta a bar kallo ce a cikin kayan, ba fara ce tas ba, amma haskenta mai kyau ne da ɗaukar hankali, domin kuwa jikinta kamar ƙwai, dan tana kashewa Jikinta kuɗi ba kaɗan ba, ba ta da wata damuwa, ba abun da take yi da kuɗi, ban da sayen kayan gyaran jiki, ta samu kuɗi a aikinta, major ya bata, Nasir ma ya bata, ga wanda take tatsar samari, ga ƴan sana’ointa, dan haka kuɗi sam ba matsalarta bane ba.
Barrister Naja’atu Bunkure matashiyar lawyer, mai dakawa maza gumba a hannu, karo da ita sai lawyern da yake jin kansa ya isa, dan abu ne mawuyaci case ya shiga hannunta ba ta yi wining ba. Ana yawan sanar da ayyukan alkhairin ta, a gidajen rediyo na taimako da tsayawa marasa galihu a kan shario’i daban-daban.
Bakin Nabila ya ƙi rufuwa, ganin yau ga ta ga Barrister Naja bunkure, wata ƴar gayu da ita, yadda ta gabatarwa da kotu kanta kawai, ya isa ka tabattar da ta san me take yi, ga yaren nasara a harshenta wato turanci.
Gaba ɗaya hankalin Nabila ba ya kan shari’ar, yana kan bunkure, da yadda take magana.
Murna kamar nabila ta taka rawa, yau ga ta ga mentor ɗin ta.
Sumayya ta samu damar editing news yau da kanta, kasancewar MD yana ta mitar, ta daina ware kanta, ta din ga shiga ana aiki da ita a haka za ta goge.
Kiran Nabila ta gani, dan haka ta ɗaga ta ce “Kiran me ki ke yi mini ina aiki?”
Sama-sama ta din ga jiyo numfashin Nabila, muryarta ƙasa-ƙasa ta ce “Kin tashi daga aiki ne?”
“A’a menene meyafaru?”
A galabaice ta ce “Na dawo chamber ne, na ɗauki kayana, ina hanyar komawa gida, ji nake kamar ciwona ne zai tashi, ina titi dan Allah Sumy ki zo”
“Subhanallah, gani nan zuwa amma babu wani a wurin da zai kai ki gida?”
“Ni ba na son damun kowa, dan Allah besty ki zo, kar na mutu a titi”
Ganin ta gama abun da take yi, ya sanya a gurguje ta ɗauki jakarta, ta fita, ba ta tsaya ko ina ba, sai hanyar wurin aikin su Nabila, tana ta rarraba ido a titi tana kiran wayarta.
A kan wani tudu ta hango Nabila, idanunta sun yi jawur, da alama tayi kuka sosai da sosai.
Ta ce “Mai napep, bari na ɗauketa ka kaimu gadon ƙaya dan Allah, ba ta da lafiya”
Ya ce “To shikenan” ta sauka ta rungumo Nabila, ta taimaka mata, ta shiga napep ɗin, sai dai babu baki, sai numfashi take sama-sama.
“Arfa, meyafaru an ɓata miki rai ne?” Ta girgiza kai alamar a’a.
“To menene? Haka kurum ciwon ya tashi” buɗe baki ta yi, da nufin yi wa sumayya masifar ta ƙyaleta, amma ta ji numfashin ta, zai gudu ya bar huhunta, hakan ya sakata yin shiru.
Can kuma a hankali ta ce “Sumayya mu je gidanku, wurin umma”
Sumayya ta jinjina mata kai, haka aka yi.
umman sumayya na ganinsu hankalinta ya tashi, Nabila ta samu wuri ta kwanta.
Umma ta ce “Sumayya, me aka yi mata ne?”
“Wallahi umma ban sani ba, kawai kirana ta yi a waya, ciwonta ya tashi”
Cikin kuka Nabila ta ce “Umma dan Allah ki yi mini addu’a, ki ƙyale sumayya”
Umma ta ce “To shikenan” ta din ga tofa mata addu’a, har aka samu ta yi bacci.
Bayan awa ɗaya da rabi, ta farka, har ta samu ta ci abinci ta yi salla, umma ta din ga tambayarta, ko wani abun aka yi mata, amma ta ce a’a.
Ganin ta ware, ya sanya umman basu wuri, Sumayya ta sake kallonta ta ce “Ke, wallahi wani abu aka yi miki, yanayinki ya nuna mini, kin ga idonki kuwa, ki gaya mini menene?”
Tayi ajiyar zuciya ta ce “Sumy, ashe haka ake ji, idan aka wulaƙanta mutum mussman a gaban jama’a, a dizaga ka”
“Menene? Waye ya wulaƙanta ki?”
Ta ɗan yi shiru sannan ta ce “Kin san Naja’atu Bunkure?”
“Ba dole na santa ba, a wurinki na santa ai”
“Ashe matar nan tsinanniya ce”
Da sauri sumayya ta ce “A’uzubillahi, me yayi zafi, mentor ɗin taki?”
Nabila ta ce “Zilwajahiani ce, abun da muke ji a kanta daban, yadda take daban. Yau muka haɗu a kotu, kin san ina cikin team ɗin barrister Bashir, tare muka je court yau.
Bayan an fito, jiki na tsuma na bita, ƴan jarida sun baibayeta, na yi mata magana kin ga wulaƙantaccen kallon da tayi mini? Ba shi ne ya dame ni ba, duk da uniform ne a jikina, na cire girman kai na gabatar mata da kaina, a matsayin lawyer mai koyi da ita, amma still ban isheta kallon kirki ba. Abunka da zuciya da abun da take so, na matsa tare da miƙa mata wayata, a kan ta bani lambarta, sai ce mini ta yi ba za ta bayar ba, kar na isheta da kira. Na ce mata bakomai, a matsayina na mai koyi da ita, kuma mai ƙaunarta, dan Allah ko mintuna uku ta bani, na daɗe ina burin haɗuwa da ita. Ina son ta bani shawara a matsayina na lawyer mai tasowa, kuma ta bani tips da zan bi, na zama kamarta a rayuwa, dan ina son ta da irin ayyukan da take yi. Ta ƙare mini kallon baki isa ba, sannan ta ce ‘Ki zama kamar ni kuma? Taka matsayin da na taka? Never! Don’t even give a try, ba zaki taɓa zama ba, and leave my way please, ina da abun yi”
Haka fa ta ce mini, a gaban mutane da masu yi mini dariya, da masu yi mini Allah ya ƙara wai neman suna da gidin zama ne ya janyo mini, wasu kuma su ka bani haƙuri wai haka halinta yake. Sumayya yau na tozarta, an wulaƙanta ni, duk yadda nake ganin ina da class, soyayya ta rufe mini ido, saboda ina ƙaunar matar nan fisabilillahi, wallahi da ƙyar na ƙarasa chamber, nan da nan na fara jiri, numfashina ya fara sama, kin ga dariyar da aka yi mini, wallahi na muzanta fiye da tunaninki”
Sumayya ta ce “Nabila jikina yayi sanyi, ban taɓa zaton matar nan za ta aikata haka ba, wai meyasa mu mata, galibin mu ƴan baƙin ciki ne? Wato ba zaki zama kamarta ba, sai ka ce wayo da dabararta ne suka ba ta matsayin da take kai”.
“Wallahi sumayya, ko zan rasa raina, ko da kasada, sai na tabattar da na yi suna nima, sai dai idan Allah ya ƙaddara na mutu. Amma ina roƙon Allah, in sha Allah tana raye, sai na ɗaukaka fiye da tunaninta, kuma bibiyarta zan din ga yi, da bibiyar duk wani abu da ya shafe ta, sai na rama abun da ta yi mini. I will do a background check on her”
“Ke fa baki iya ɗaukar abubuwa da sauƙi ba, ki ƙyaleta mana kanta ta yi wa, ni na ce me?, abun da nima ake yi mini, ni kusan kullum ake yi mini, ke yau ne kawai, kuma arfa matsayi na duniya ba na kiyama ba”
Nabila ta girgiza kai ta ce “Wannan ke ki ka ga zaki iya, kuma ƙaramar alhaki ce ta wurin aikinku, wannan kuwa dizgin da ta yi mini, in sha Allah rabbi, sai na rama shi, dole na ajiye shirme, na mayar da hankali a kan aikina, ko dan fansar nan, kut wallahi matar nan ta gama cuta ta, kuma ba zan huce ba har sai na rama wallahi. Rakani titi in tafi gida” ta ƙarasa maganar tana ƙoƙarin tashi tsaye.
Sumayya ta danƙota ta ce “Nabila ki din ga sanyawa zuciyarki salama mana, kin fiye zafin rai, ki bi komai a hankali, kalli yadda ki ka kusa kashe kanki a banza. Idan Allah ya yi nufin ɗaukakaki fiye da ita, ita ɗin banza ta hana, dan Allah ki manta da ita, ki cigaba da rayuwarki”.
Ta kalli sumayya cikin takaici ta ce “Lallai ma sumayya, dan ba ki ga abun da ta yi mini ba, a gaban mutane har da masu yi mini dariya. Ni gaba ɗaya ma ji na yi ban yarda da ita ba, abun da ake faɗa a kanta daban, abun da na gani yau a kanta daban, akwai wani abu a ƙasa, and i will run a background check on her, for the first place ma, wacece ita? Idan ta kama har bunkuren zan je mahaifarta, meyasa abun da ake faɗa a kanta daban, ita kuma halinta daban”.
Sumayya ta ce “Na shiga uku, Nabila” kafin ta yi magana, Nabila ta yi waje, ta tarar da umman sumayya na salla, ta ce Umma na tafi, ta fice daga gidan.
Sosai abun da ya faru ya tsayewa Nabila,da ta tuno abun sai wani irin takaici yakamata.
Yau ba kowa ya san ma ta koma gida ba, dan yau babu surutu da hayaniya.
Abu kamar wasa, har dare Nabila ta kasa walwala, ko fitowa daga ɗaki taƙi yi, gani take kowa yana kallonta zai gane an dizgata yau, duk iyayin na ta da jan ajin.
Nabila irin mutanen nan ce masu saka abu a ran su, dan haka ko ta yi niyyar manta abun da ya faru, sai ta kasa.
Ta ɗaukko wayarta, ta kunna data, ta tarar da messages ɗin sumayya, ta na ta yi mata faɗan ta yi haƙuri ta manta da abun da ya faru.
Nabila ta yi mata reply da “You are not serious, ki saka ido ki yi kallo”
Social media ta hau, ta shiga searching ɗin sunan barrister Naja’atu Bunkure, nan da nan sai ga hotunanta, da wasu daga cikin ayyukanta na jin ƙai, sai dai ba ta samu wani cikakken bayani da take son samu a kanta ba.
Tsaki ta yi, bayan tuna yadda take mutuwar son matar nan a baya, har hotonta take sakawa a dp ɗin ta, saboda yadda take ƙaunarta, amma lokaci ɗaya a yanzu ji take yi, ba ta da wani maƙiyi idan ba ita ba.
Har sha biyu da rabi na dare, ba ta samu cikakken abun da take son sani ba, sai ma zarge-zarge da suka din ga ɗarsuwa a ranta game da matar.
Saukkowa ta yi daga kan gadonta, ta fice daga ɗakin, fita tayi can babban falo, ta nufi kitchen ta samu abun da za ta ci, dan yunwa take ji sosai.
Fridge ta buɗe, ta samu ruwa mai sanyin gaske, da coc ta fito falo tana sha.
Hasken fitila ta hango a baranda, ba a kashe ƙwan wurin ba, ga abba kullum sai yayi magana a kan rashin kashe kayan wuta, kafin a kwanta bacci.
Wurin ta nufa, da niyyar ta kashe ƙwan, ta na zuwa ta leƙa, ta hango nasir a kan kujera, yana ta danna system.
Ta window ta je ta zura hannu, tana taɓa masa kunne. Caraf! Ya riƙe hannun ba tare da ya ɗago ba.
Tayi dariya ta ce “Shi ne ba ka tsorata ba”
“Me ki ke tunanin zai razana ɗan sanda?”
Ta ce “Ai dai ɗan sanda mutum ne, kuma na san ka ji tsoro mazewa ka yi”
Yayi murmushi ya ce “Tsoro sai lauyoyi”
Ta buɗe ƙofa ta fita ta zagaya in da yake ta ja kujera ta zauna sannan ta ce “Duk tsoron lauya bai kai ɗan sanda ba”
Ya ɗago ya kalleta, sanye cikin kayan bacci pink, masu bargo kanta ko ɗan kwali babu, tayi parking ɗin gashinta”
Murmusawa yayi ya ce “Ke kin san babu tsoro ga wanda yake riƙe makami, yayi yaƙi da ɓarna”
“Hmm, yi dai a hankali, dan harshe ya fi makami dafi, kar lauyoyi su baka mamaki watarana”
“Ina aiki kin zo zaki dame ni, ina nawa aikin, ina kallabinki?”
“Yana ɗaki” tayi maganar tana lashe murfin jarkar lemon hannunta.
“Kalli abun da ki ke yi kamar ƴar ƙauye, sai an yi magana ki fara ke barrister ce, ke degree holder ” yayi maganar yana mayar da hankali a kan system.
Ta numfasa ta ce “Wai aikin me ka ke yi ne?”
“Wani aiki ne mai wahala, wanda nasara a kansa, na iya sawa na samu cigaba a aikina”.
Nabila ta ce “Haba dai, to Allah ya taimaka”
“Amin” ya amsa ba tare da ya kalleta ba.
Shiri ya wanzu na wani ɗan lokaci, sannan ta ce “DSP”
“Na’am barrister”
“Sannu da aiki” ya ɗago ya kalleta ya ce “Kin isheni fa, za ki tashi ki bar wurin nan”
“Yi haƙuri, na daina magana”
Ya cigaba da aikinsa, ta na shan lemonta, tana jin yadda iska ke kaɗata.
Duk abun nan, Abba ta ɗakinsa ya na hango su, sai dai ba ya jin me suke cewa.
Can ta sake cewa “DSP”
A hasale ya ce “Ke! Meye ne? Tashi ki je ki kwanta dare yayi”
“Ni na kasa bacci, raina ne a ɓace”.
“Ai dama kullum cikin ɓacin rai ki ke, tun da ke a rayuwarki ta duniya, baki da haƙuri tashi ki bani wuri”
Ta marairaice ta ce “To ka tsaya ka ji me aka yi mini mana, dan Allah kafin na tafi, ka gaya mini me zan yi, wanda zai saka na yi suna, kowa ya sanni” tayi maganar very serious.
Cikin gatse ya ce “Ki nemo in da Aminu Viper yake, ki taimaka mini na kama shi, kin ga sai ki yi suna, ni na samu cigaba a aiki”
Ta fuskance shi sosai ta ce “Waye shi, a ina yake? Kamar na taɓa jin sunansa”
Ya kalleta ya ce “Shi nake ta aiki a kansa, galibin aikin ta’addancin da ƴan daba suke yi, a wasu shiyyoyin da saka hannunsa, yaransa ne. An ce lallai na kamo shi, tun da yankin da ake ɓarnar ƙarƙashin kulawata yake akwai zarge-zarge a kan guduwa yayi daga prison”
“Dan Allah idan na nemo maka shi, zan yi suna, kowa ya sanni?”
Kallon baki da hankali yayi mata, ya cigaba da abun da yake yi.
“Ka ga riba biyu kenan, na yi suna, kuma ka samu cigaba a wurin aiki, yes! Amma na ji ka ce akwai zarge-zarge a kan guduwa yayi daga prison how? Kun tabattar da hakan ko kuwa? Ka bani hints mana, laifin me ya yi a ka kai shi prison ɗin?”.
Takalminsa ya ɗauka ya miƙe tsaye ya ce “Tashi ki bar wurin nan, tashi maza”
Da haka ya koreta, ta tafi ɗakinsu. Sai dai da ga koma ɗakinta, ta dinga sintiri a cikin ɗakin, sosai ta ji maganar Yaya Nasir ta shiga ranta, ina ma hakan ta tabatta.
“In taimaka masa ya kama ɗan ta’adda, in nemo haƙiƙanin dalilin barinsa daga gidan yari, idan guduwa yayi me ma’aikatan suke yi, idan sakinsa aka yi laifin me yayi, aka sake shi duk da hatsarinsa, na bankaɗo ainihin identity ɗin Naja’atu Bunkure, na gyara career ta, wai ma menene dalilin da ya sa ban zama ƴar sanda ba?, na zama wata lauya yau ka kare mai gaskiya gobe mara gaskiya.
Ta yi wani irin shu’umin murmushi ta ce “Accepted DSP Nasir, zan nemo maka Aminu Viper, na bibiyi laifin da ya aikata, da yadda aka yi ya bar prison.


