Littafan Hausa Novels

Zaki Hausa Novel by Khadija Candy

Written by mynovels

Zaki Hausa Novel by Khadija Candy

 

 

 

 

 

 

 

 

*Z A K I*

 

By Khadeeja Candy

 

1️⃣

 

Carar Zakaran dake harabar gidan ne ya katse min dogon bachin da nake. A hankali na matsa fuskata dauke da murmushi domin ko kadan hakan be bata min rai ba, na daga hannuna a sama ina mika tare da kara watsakewa, kamar kullum yau ma bachin ya min dadi, ba dan gurin da nake kwanciyar ba, sai dan farinciki da kwanciyar hankali da natsuwa irin ta masu wadatar zuci data cika min zuciyata nake kwanciya da ita a kowane dare.

Kamar wacce akai wa dole haka na bude manyan kuma lussasun idanuwana da suka rine suka sauya kala sakamakon dadewar da nai ina bachin. Akan farinciki na sauke idonuwana wato mahaifiyata wacce ke sanye da wani jan yade kodadden irin na talakawa kuma na gadonmu.

 

“Wainar ki ce take ci tun dazun aka aje miki”

 

Da yaren buzanci mahaifiyata take muna min kyanwar dake kusada ni tana cin waina.

 

Murmushi nai na kai hannuna na shafa kyanwar kana na shiga mata magana da yaren buranci.

 

“Kin cinye min waina ko?”

 

“Ataa yau ba za ki je baranki ba ne?”

 

Kanane ya tambaya, hakan yasa ni saurin tashi daga kwancen da nake, na fito daga cikin bunkar ina hamma ba tare dana rufe bakina ba, ba dan kuma ban san babu kyau ba, sai dan rashin kula da watsi da addini irin na mu na… Da hanzari na nufi wani dan guri da muka killace da kwano domin yin wanka ko kuma ba haya. Ba wanka nai ba domin wanka be dame ni ba duk kuwa da kasancewar na fi kowa tsabta a cikin gidan mu amman a hakan sai na kwana uku ban yi wanka ba.

Fitsari kawai nai na fito da sauri na wanke fuskata da fassashiyar butarmu marar murfi, sai da na gama wanke fuskar sannan na nufi gurin da muke girki na dauki gawayin kara na saka a bakina na tauna na saka yatsana na wanke bakin na kuskure sannan na wanke kafafuwana na nufo bukkarmu da sauri tuna ban yi sallah ba yasa na dawo na dauki butar nai alwala na sake kowa bukkar wanda zan iya kiransa da dakinmu.

Zanen dake daure a kirjina na cire na dauki riga da wando na wani shudin yadi mai kamar laile na saka na dauki hijab na saka nai sallah mai kamar asha ruwan tsuntsaye, wato da sauri domin cikin kannanen lokaci na yi na gama. Bakin dankwali na dauka na cire hijab din kaina na saka bakin dankwalin mai kama da karamin gyale na rufe kaina kamar yadda na saba ko kuma na ce muka saba.

 

Na kai hannu na dauko madubi tare da gawayin dana daka na kwaba tare da man shafi a guri daya, tsayawa nai kallon kaina a madubin ina murmushin daya kara bayyanar da kyauwona har dimple dina suka bayyana, sai faman lumshen manyan idanuwana nake ina budewa. Abu ne da ya ke bayyane, bana bukatar kowa ya kalleni ya fada min cewar ina da kyau, kyau na hali ko na halitta kyau na jiki ko na fuska, ni kaina idan na kalli madubi kyawona tsorata ni yake, idan ba a kirani balaraba ba to ba za a cireni a jinsin india ba indiyawan ma sai an tona, hakika ni kaina na san ina da kyau na wuce misali, kyan dake hana ni shakaf a cikin al’umma, gashin kaina kadai idan na sake ya sauko mutune har mamakin yadda nake da yawan da tsohon gashin dake saukona har mazaunaina suke.

Ba sai na fada ba, duk wanda yasan jajayen buzaye yasan su da kyau da gashi sai dai a cikinsu ni din ma ta dabam ce a bangaren kyau. Man dake gabana na gawayi na dauka na shafa a fuskata a take farin fuskarta da kyau ya gushe na koma kamar ba ni ba, dogon hancina kawai zaka gani ka iya gane ni shima kuma sai idan ka sanni farin sani sosai.

Sannan na mike tsaye na dauki kwagirin dana saba ratayawa a koguna (kwankwaso) idan zanje yawon bara na daura. Gurin da mahaifiyata take zaune naje ina mata sallama da yaren buzanci.

 

“Na tafi Nana”

 

Haka nake kiranta da sunan dana tashi naji mutane na kiranta da shi duk kuwa da kasancewar ba shine aihanin sunanta na gaske ba.

 

“Allah ya tsare a samo da yawa”

 

Ta fada min tana dariya ni kuma na kada kai na fice ina murmushin domin bata san gaskiyar abun ba, a duk tsawon kwanakin da nai ina aikin.

Sai da nai nisa da bukkarmu ta yadda babu wanda zai iya hango ni sannan na ra6a ta cikin kangon gidan da muke gaban bukkar mu wanda wani shahararren mai kudi yake ginawa na shiga ta gurin da aka fasa domin yin windows na fada cikin wani gurin da ban san me za ayi da shi ba, daki ko falo, na dauki kayan aikina na bi ta kofar gaba na fice, na saba ba tun yau ba, idan nai nisa da gidan mu da sunan zuwa bara kamar yadda mahaifiyata take saka ni sai na biyo ta window kangon gidan na dauki kayan wankin motana, na bi ta kofar fita na fito, har yau mahaifiyata bata ta6a sanin cewar ina wannan aikin ba, ni kuma ban ta6a ganganci fada mata ba, domin na san zata hana ni idan ta gano ba bara na ke ba, kamar yadda take son nai, ni kuma bana son barar domin tana ci min rai, kamar yadda take kankantar ni ga duk wanda na mikewa hannu na ce ya bani.

Ya zame mana kamar al’adar yin bara a titi ko manyan gidaje ko ma’aikatu domin samun abunda zamu ci, wasun mu suna da shi wasunmu suna da rufin asirin da zasu iya rike kansu ba tare da sunyi bara ba, tsabanin mu da kullum sai mun yi bara muke samun abunda zamu ci. Na sha ganin irin wulakancin da ake ma mahaifiyata kala kala idan muje bara musamman akan titin manyan motoci wanda hakan yake bakanta min rai, sai dai ita ko a jikinta duk kuwa da irin kyamar da ake nuna mana.

Wannan dalilin ne yasa na daukar mata alkawarin cewar zan rika yin bara da kaina ina kawo mata kudi ita ba sai taje ba, da wannan ta dogara ni kuma na sauya hanyar bara zuwa neman na kai, duk kuwa da kasancewar wasu na min dariya ganin kamar aikin be dace da ni ba, wai ace mace kamar ni ina tsayawa a inda motoci ke tsayawa saboda traffic ina wanke gilashin mota ana biyana, aikin da akasan maza ne suke yi. Nikam hakan be taba damuna ba, domin na san yafiye min bara kuma ina samun sosai fiye da baran ma, ganin ni macece yasa wasu mazan ba hansin suke ba ni ko ashirin ba, har dubu daya na kanyi dacen wani ya bani.

Ba dan kuma an san ni din wacece ba, domin kullum fuskata shafe take da fantin gawayi wanda hakan kan jama min kyama a gurin wasu, sai dai ni yafi min kwanciyar hankali na boye kyauna na, gudun abunda zai iya biyowa baya, za a iya kawo min hari kamar yadda aka sha min lokacin da muke wacan gidan da ba a tashe mu ba, duk wanda ya kalle ni a aihinin yadda Allah ya hallicce ni ba za a min kallo daya a dauke ido ba, ba kuma za a ki fadar cewar ina da kyau mai jan hankali ba, mata ma sukan fada balle mazan da babu adadi.

Ko a unguwar da muke zaune a yanzu wato Clapperto babu wanda ya san iya ainahin yadda fuskata take, domin kullum ina tare da bakin gawayi a fuskata, wanda hakan kan sa a kara kiranmu da kazamai, ganin irin gurin da muke zaune mai kama da juji, wani kangon fili ne kato wanda aka ware wani bangare na filin aka fara ginin gida kuma aka bari, lokacin da aka tayar da mu daga wacan kangon gidan da muke rabe sai muka dawo wannan muka zauna ba tare da tambayar izinin mai shi ba, muka kafa yar bukkarmu muka zauna a nan muke rayuwarmu ta yau da kullum.

 

Na saba tafiyar kasa, dan haka komai nisan guri ni baya damuna, ina tafe ina rare wakar mu ta buzanci wance mahaifiyarmu take yawan rarewa a gida, idan na dora alkalamina a ko wane kalar littafi zan cika shine da kalmar kaunar iyalina kamin na bayyana komai na rayuwata, ina son yan uwana kuma ina son yarena da al’adata fiye da komai a duniyar nan.

 

A sannu nake tafiyata har na iso babbar flyover din Alu inda na saba wanke motoci ana biyana, kamar kullum mutane suna ta kai kawo a gurin kama daga masu babura da masu napep da kuma masu motoci manya da kanana. A cikin a kusa na soma sana’ata idan naga babu motoci sai na koma inda muke zama ni da abokanin sana’ata yara maza mu zauna sai idan an sake hada motoci sai muje da gudu mu wanke wasu kuma suna siyar da popcorn wasu kuma pure water, wasu air freshener da turare dai sauransu.

 

Sai da yamma lis na nufo gida gani a gajiye amman ba zan iya cire kudi na hau abun hawa ba, a ganina idan na hau kudin zasu ragu, kamar yadda mahaifiyata ta koya tun a lokacin da muke bara.

A hanya na siye pure water da gyada ina tafiya ina ci can ta tsallaken titi nake hangon wasu buzayen irina a jikin wata motar suna mika masa hannu ya basu, ni dai ban da kallonsu babu abunda na ke, ban ankara ba naji an watso min ruwan saman da akai kwana biyu da suka wuce, wadanda suke kwance a gefen titin sakamakon wucewar da wata motar tai da gudu kamar zata tashi sama.

Wani bakin haushi naji domin ba kadan ruwan da motar ta taka suka bata min tufafi ba da kuma kayan aikina, dan brush da man wanke mota da kuma kyalena na gogewa idan na wanke.

 

Bance komai ba naja tsaki na cigaba da tafiyata, yo daman wa zance wa wani abu tunda ni kadai nake ta tafiya ta. A natse nake tafiya ta har na karyo kwanar dana saba bi idan zanzo gida, ina yanke hanya ne domin abun ya zo min da sauki, sai dai duk da haka ana kiran magariba na soma dosowa unguwarmu ta Clapperto road, a dai dai bakin gate din gidan dan Uti idanuwana sukai arba da kalar motar da wuce ta gabana dazun ta bata min tufafi, kuma wani abun dadi babu mutane a titi sai karar motocin dake kai da kawo.

Kida A Ruwa Hausa Novel Complete

Sai da naje gaban motar na leka gaba babu kowa a ciki, sannan na kara matsawa ina kara tabbatarwa idan ita dince ko aa, kalar dai daya ce sabuntar ma daya ce sai dai wannan anyi mata hoton ZAKI a jikin number motar kuma an rubuta mata ZAKI 001 da manyan haruffa tsabanin wacan da ban kula da number motar ba ma balle ma na san me aka rubuta.

Komawa nai ta inda na fito ina ta kalle kalle har na hango wani katon dutse da be fi karfina ba, na dauko na zo na jefawa motar ta gurin gilashinta, a take ta fara kuka, ni kuma na ranta cikin na kare, ai daman dai burina na dauki fansa, ko ba shine ya bata min tufafi ba be dame ni ba dan dan’uwansa ne mai kudi sai suji yadda ake ji…

Abunka da marar jiki nan da nan na karya kwana kwana ina ta sauri kamar an biyoni, tsoro ya saka na kasa mikewa kai tsaye na bi titi na isa gida, sai na shiga ta hanyar gidan taba (Gidan azaba) na bulla ta can kwantagora road na karyo ta wata hanyar, domin kawai wahala sannan na bullo da gidajen yan sanda da yake nan na biyo ta bayan gidan Alkali Abu dange wato gidansu Khadeeja Candy na fito titi Clapperto road na doshi gidanmu.

 

A inda na saba aje kayana na nufa na aje sannan na fito ina kirga kudin dake jakata, kamar ance na waigo ko da na juyo sai na hango wata halitta mai kyau da daukar hankali da kuma ban tsoro tana kallona. Mutum nake hange amman a siffa da fuskarsa, sai dai kwarjininsa da aibarsa kamar wani zaki. Nesa yake da ni amman fuskarsa zooming take min tana kawo min shi kusa kamar yana tsaye a gabana. Annuri ne shimfide a fuskarsa, sai dai ba irin na masu dariya da sakin fuska ba, irin wanda annurin ya zame masa jiki yake bayyana kansa a duk lokacin da mai shi ya kalleka, kwarjinsa ya cika min ido har kure ganina nake ganin kamar daga ni sai ainahin Zakin ne a jeji, wani abu mai zafi naji yana bin kafafunawa, ashe fitsari nake a tsaye ban sani ba, tsabar tsoro ya cika min ciki sai na fadi zaune a gurin na rufe idona kunya ce ta kamani budurwa kamar ni ace tai fitsari sai kuma naji ashe ba kunya ba ce tsoro ne…..

 

 

__________________

 

Who’s ready for the next chapter?

 

#ZAKI

#Vote

#Share

#Comment.

 

 

Thanks Share Pls🙏🏻

*Z A K I*

 

By Khadeeja Candy

 

 

2️⃣

 

Mafarin ko wace Rayuwa numfashi da jini ne, ne numfashin da nake fitarwa ne ya tabbatar da cewar a raye na ke. Sai dai bana iya tantance yadda nawa numfashin yake a yanzu, domin surkinsa da wani kalar iska ne mai dadi shaka. A take na bude idona sai na hango gurin da mutumen yake tsaye kamar anyi ruwa an dauke domin babu alamarsa balle shi din yayi batan dabo bat kamar be taba wanduwa a gurin ba. Wata kila yaji tsoron fuska ta ne dake da bakin gawayi ko kuma rufen idon da nai ya tsorta shi, shiya saka yai hanzarin barin gurin.

Samun kaina nai da murmushin kaina saboda tsoron dana ji, na Lumashe ido ina shakar kamshin turare mai shiga har cikin kwakwalwa ya samawarda natsuwa ga marar ita ga mai ita kuma ya dada masa.

Na risina na dauke kudina da suka zube ina dariyar kaina, domin sai a yanzu abunda nai yake bani dariya na fashe gilashin motar mutane saboda mai motar ya watsa min ruwan kazanta a jiki, wata kila ma ba shi yai ba.

Lokacin dana hango mahaifiyata tana a gaban murhu sai farinciki da jindadi ya lullube ni, domin ba kasafai zaka zo ka tarar an dora girki a gidanmu ba, mun fi siyen garin kwaki mu jika ko muyi kwado (Datu) da kuli mu ci, idan wadatar tai mana yawa muna siyen kanzon tuwon dawa ko na shimkafa mu aje muna ci, hakan yasa na iya sarrafashi ta ko wace siga, idan nai jalof dinsa sam ba zaka ci ka dauka cewar kanzo ka ci ba har sai idan na fada. Ban saba shiga gidanmu da sallama ba, dan haka yin sallamar be dame ni ba sai kawai na karasa gurin mahaifiyata ya kai hannu na bude tukunyar dake kan wuta ina fadin.

 

“Nana me kike dafawa”

 

Ba shiri ya yada murfin sakamakon wani azababen zafi da naji a take yan yatsuna sukai ja, sai dai ganin taliya yasa ni manta zafin dana ji duk kuwa da irin halina na raki sai wani farincikin ya kara baibayeni har na hade yawu. Ina son taliya sosai musamman dafuwar masu kudi ba irin tamu ba da sai an sauke muke saka yaji da magi wani lokacin ka gishiri kawai za mu saka mu ci.

 

“Taliya ce nake dafawa”

 

Ta bani amsa itama fuskarta dauke da far’a.

 

“Ina kuka samu kudi?”

 

“Bayan fitarki Maman Maryam ta aiko mana da ita”

 

Na yi dariya ina saka hannuna a kwagirina dake kuguna na ciro duk kudin da nai na mika mata, ban san na rage ba balle har na cire wani abu ko da kuwa ina da bukatar siyen wani abu ne, har sai idan Nana ta dauka da kanta ta bani. Gaba daya kudin da nai a yau ba su wuce dari uku da yan canji ba, daman ba ko wace rana ce jumma’a ba.

 

“Wai Ataa ina kake zuwa baran ne? Kullum kudin da kake samowa be wuce wanda za si abinci da safe ba, da rana haka muke wuni babu komi a ciki inda ba Allah ya kawo mana wani abun ba”

 

Na yi shiru domin ban san me zan fada mata ba, tana da gaskiya a lokacin da take baran tana tara kudi mai yawa har ma ta siye wani abun ta aje, tsabanin yanzu dana hanata kuma ni bana iya kawo abun kwarai domin ni ba baran na ke ba.

 

“Nana kin san ni ban iya baran sosai ba, kuma bana son zuwa gurin manyan motoci ba”

 

“Ka gani Ataa ka cire wannan girman kan, ka raba kanka da girma kai ka ba dan kowa ba, idan za ka dage ka yi bara ka dage domin shi ne komai na mu”

 

Fada take min amman dariya nake, saboda yadda take kirana namiji kamar yadda take yi ma ko wace mace idan kuma namijin ne sai ta mayarda shi mace, domin ita har yanzu hausarta bata gama fita ba. Sai itama tai dariya domin ta san abunda nake yi ma dariya.

Daga haka na samu na shashantar da maganar na tashi na dauki fassashiyar butar mu na zagaya a inda muka killace na wanke fitsari sannan na fito na saka sabulu na wanke fuskata mai bakin gawayi nai alwala na shiga bukkarmu. Ban samu kanena Lukman a bukkar ba hakan ya tabbatar min da cewar yana islamiya kenan. Iyakar kokarin da nai na canja tufafin jikina ne na saka wasu sannan na soma rama azahar kamin na dora da la’asar. Ba tozarci ba, ni kadaina ina shakkar sallah da muke a bukkarmu domin na taba ji a lokacin da nake zuwa makaranta ana cewa Allah baya karba sai mai tsarki sai dai ban iya banbancewa ba tsarki na fitsari da janaba ko kuwa tsarki irin wannan na tsabtace daki. Babu wanda zai iya zama dakin mu yai minti biyar a ciki saboda zarnin fitsarin Lukma da kuma na kayan daudar da suke bukkarmu ga tarin kwanoni marasa marafe da kuma tarin gwangwayen da Nana take tarawa wai idan suka kai buhu uku zata siyar.

Ina sallamewa kunnuwana suka sato min muryar Lukma dake fadin.

 

“Nana kin dawo gurin baran?”

 

Juyo nai da sauri ina kallonsu daga inda nake zaune, daga ita har kanena basu san ina yi ba.

 

“Nana bara kike zuwa?”

 

“Ataa idan be je bara ba, da me zan dafa taliyar nan?”

 

Daga can gaban murhun ta amsa min kai tsaye. Wani abu na ji ya tsaya a kirji wanda ya saba tsaya min a duk lokacin da mahaifiyata taje bara.

 

“Amman Nana na fada miki zan rika yi ba”

 

“Ba inda kake zuwa kake zuwa (Nake) kai wani guri kake tafiya dabam”

 

Na turo baki baki ina bata fuska. Har tai girkin ta gama ni fushi nake ta yi dan taje bara sai dai hakan be hana ni cin taliyarba, sai dai ni sai da naje na siyo man kuli na zuba sama da yaji sannan abun ka da mai kwadayi baki baya son ba dadi.

Washe gari ma kamar ko wace rana sai da haske rana ya leko bukkarmu sannan na farka daga bachi, a maimakon na tashi sai na kara dunkulewa cikin wani tsohon zanen gado wanda rabinsa ya gama yagewa (Barkewa). Bana jin yau zan tafi aikin dana saba zuwa da sunan bara, inda har zan je nai abunda zai kare mutumcin mahaifiyata ita kuma ta zaga baya idona taje bara banga amfanin zuwan nawa ba. Dan haka ban fito daga bukkarmu ba sai kusan tara da rabi duk da kasancewar babu agogo a bukkar balle na iya ganewa sai dai a yadda na auna tara tayi ko ma ta dan gota. A lokacin ne na dauki butarmu na zagaya can nesa da bukkarmu a wani fili da aka ware ban san me za ayi da shi ba, a nan na saba yin ba haya ta a duk lokacin da bukatar hakan ta kamani, domin a wacan gurin da muka zagaye da kwano da sunan bandaki idan mukai ba haya a ciki sai mun kwashe mun kai can nesa mu zubar a kullum ni kuwa zubarwa ne yake bata min rai, na zabi nai nesa da bukkarmu nayi bahayar a inda aka tana da domin yin wani abu.

 

Bayan na gama na dawo na saka kasa na wanke hannuna sannan na saka sabulu, sai kuma na dora da alwala sannan na shigo dakin nai sallah asuba. Da yaren buzanci mahaifiyata ta fada min cewar na dauki waina mai kuli na ci na tashi muje bara.

 

“Ni bana son zuwa bara Nana”

 

“Sai ka je, gaba daya zamu je”

 

Haka na turo baki na bata fuska sosai kamar zanyi kuka, amman hakan be saka ta kyaleni ba, har sai da na ci wainar ina ta fushi daya kasa boye kyawon fuskata, har sai ta na dauki bakin gawayi da mai na shafe fuskata da shi sai gani na fito wata mummuna kamar ba ni ba.

 

“Kin fi son ki shafa bakin gawayi kullum a fuskarki kamar wata dodo”

 

Mahaifiyata ta fada da yaren buzanci, daman can tafi kowa tsarguwa da shafa gawayin da nake domin yafi min kwanciyar hankali da lamana. Ko ba komai hakan hana sa ana min kallon kazama wanda ba karamin kariya yake min ba, na san da ace yan iskan mazan da suke unguwar za su ga ainahin yadda fuskata take wata kila da ace cikinsu wani ya keta min haddi….

 

 

Cikin rashin maida hankali na saka tufafin jiya masu kama da farin lela na yafa bakin gyale kamar yadda yawancin buzaye suke yi, mahaifiyata kuma ta yafa fari wanda ya gama dafewa ya canja kala saboda tsufa da kuma lalacewa. Lukman ya dauka yar robar ruwansa da kuma ta bara kamar yadda ya saba Nana kuma ta dauki ghana must go dinta ni kuma na daura jakata (kwajiri) a kuguna sannan na dauko wani tsohon gidan sauro ya rufe a saman bukkarmu a daidai inda kofar dakinmu kana na dauko wano (Langalanga) na rufa a gurin kofar kamar yadda muka saba idan za mu fita unguwa. Nana na gaba ita da Lukman suna firarsu abun shawa’a ni kuma ina baya ina kallonsu har muka isa gaban manyan shagunan da suke gawon nama inda manyan motocin masu kudi suke tsayawa siyen abu. Kamar yadda muka saba a can baya lokacin da muke baran ni nakan tafi gurin wata motar dabam Nana kuma ta tafi gurin wata dabam ita da Lukman idan mun fita tare da shi, idan kuma gida muka bar shi to ni da ita a tare zamu rika bin motoci ko kuma mutanen dake shiga cikin shagunan.

Ba ma magana sai dai mu muka hannu mu marairaice fuska kamar za mu kuka ta yadda mai ba mu zai dauka ba mu da sama balle kasa ya taimaka mana.

Haka muka wuni a gurin muna ta mikawa mutane hannunmu idan ya fito daga mota ko zai shiga wani shago har muka tara da dan yawa, duk abunda mahaifiyata ta siya sai ta aiko Lukman ya kawo min na ci. A haka muke har yamma tai daf da zamu tafi gida na hango wata motar a fake da sauri na nufi motar a zatona akwai mutane ciki sai da na isa sai naga babu kowa a ciki sai dai gilashin motar a sauke yake. Ina juyowa sai naji na bugu mutum, da sauri na dago kai sama ina kallon wanda na buga din, dogo ne mai faffadan kirji mai tsananin fari ga kwarjini da haifa, duniyar kamshinsa ta tunatar da ni cewar shine dai mutumen dana fasawa mota a yanzu ma ji nai na zama wata yar tsuntsuwa, yana ta kallona da fuskarsa mai dauke da walwala kuma ba walwalar ba, ba kuma ra a kira shi da rashin walwala ba, amana dai ba yabo ba fallasa a bayyana yake kana kallonsa kasan abu ne mai hawayin ya dabbata Sunnar murmushi a addininsa. Kwalla nake saboda ainahim zatin fuskarsa da nake kallo, ba hawayen kyawonsa ne ba, ba kuma na rashin far’ar fuskarsa ne ba, na tsoro ne irin wacan tsoron daya kamani jiya a lokacin dana hangoshi tsaye yana kallona, banbancin wacan karon da wannan a jiya fitsari nai yau kuma kwalla ne a idona na tsoro da fargabar abunda zai min. Lokaci daya naji an fisgoni wanda hakan ya bani damar sauke numfashin da ban san ina rike da shi ba sai a yanzu.

 

“Yana son ya shiga motarsa kin tare nasa hanya Ataa”

 

Nana ta fada tana rike da hannuna, ji nai na dawo duniyar mutane mai cike da hancin iska. Da hanzari mutumen yai saurin cire jacket din jikinsa ya bar t-shirt saboda na dan shafe shi kadan lokacin da mahaifiyata ta janyo ji domin na bar jikin motarsa, cike da kyankyami ya bude boot ya saka jacket din ya rufe ya dawo mazaunin gaba ya zauna yana goge hannunsa da tissue paper saboda ya rika rigar dana shafi gefenta kadan.

Sai a yanzu na gane, wato duk tsayin da yake yana kallona na jiran na bashi guri ya shiga motarsa ne, amman ba zai iya yi min magana ba, wata kila maganar wahala take masa ko kuma yana kyamar furta kalmar kauce na shiga motata ga mace iri na ne….

Ni dai da kallo na bi motar sai a yanzu na lura da number motar ita ma ZAKI ne rubuce a jikinta, sai dai wannan motar ba irin wacan bace ko a kala balle a kama.

 

“Miya saki kuka?”

 

Na na ta tambaya da yaren buzanci tana nuna hawayen fuskarta. Sai na saka hannu na share na bata amsa da hausa ina turo baki kamar wata shagwa6a66iya.

 

“Tsoro na ji”

 

Dariya tai Lukma ma yai min dariya ni kuma na kara turo bakin kamar zan cireshi gaba daya…

Sai da aka fara kiran sallah sannan muka dawo gida, a yau ma yar kullum ce sai da na wanke fuskata sannan na rama sallar da ake bina kana nai sauran, Mahaifiyata akam ba a magana domin sallah bata dame ta bayan sallah asuba bana jin tana wata Sallah sai idan ta kama. Lukman Nana ta aika ya siyo mana gari da sugar muka jika muka sha, ni kuma na roki Nana naira hansin a kudin dana samo ta bani na siyama kyanwata kifi na bata, tana ci ina shafata ina murmushi ina sonta sosai domin Allah ya saka min son kyanwa musamman wannan da muka sabu wani lokacin har fita nake da ita idan zan je wani gurin.

 

Washe gari ma haka na farka raina fes zuciyata kal kamar yadda na saba farka a ko wace safiya ta Allah duk kuwa da irin rashin da muke da shi. Sai dai yau ta sha banban, dan kekasa kasa nai na ki yarda na bi mahaifiyata da taga bana son zuwa sai ta kyaleni a bisa sharadin zan je inda na saba yi nai ba tare da ita ba. Bayan ta fita nima na shirya na shiga kangon gidan nan na dauki kayan aikina na kama hanyar Flyover din Alu. Ina isa na fara aikina na wanki mota a biyani, idan na hango manyan motoci na fi saurin zuwa na wanke musu domin sun fi baka kudi tsabanin na direbobi da wasu sai dai su wuce su barka ma ba tare da sun baka komai ba, wasu kuma su samma maka abunda ya samu.

Wata fara mota mai bakin gilashi na zubawa mai na fesa mata ruwa ina gogewa kamin traffic ya sakesu, bayan na gama na dawo ta gaban gilashin motar ina jiran mai ita ya sauke gilashin ya bani wani abu, A hankali aka zuke gulashin motar sai fuskar mutumen nan na jiya da shekaranjiya ta bayyana, a maimaikon ya bani kudina sai ya miko naga an zuro min hannu.

 

“Ba ni wayar da kika sata?”

 

Hannun na mace ne haka zalika muryar ma ta mace ce, sa tsakanin ba ni wayar da kika sata da kallonsa fuskarka da nake sai na rasa wane yafi wani razanar da ni, duk kuwa da kasancewar ba ni yake kallo dan da alama ni din ma ban isashe shi kallo ba, traffic kawai yake jiran a sake ya ja motarsa…

 

 

 

____________________________

 

Yaushe Ataa ta saci waya kuma?

Wanene wannan mutumen?

Ya dandanon labarin yake a kwakwalwarku?

Akwai suga kuwa? 😃

 

#Vote

#Comment

#Share

#Zaki

https://my.w.tt/GuQH5GZKb9

 

*Z A K I*

 

By Khadeeja Candy

 

 

3️⃣

 

ALIYU POV.

 

Ana sakin traffic din yaja motarsa sukai gaba. Husna ta waiga tana hango Ataa wacce ta koma gafen titi tana hango motarsu tana jin kamar ta koma amman ba dama.

 

“Wannan ya zama na karshe i mean na last last time da sauke gilashin motata ki yi magana da wani saitin kunnena”

 

Ya fada ba tare da ya kalleta ba, tsif tai kamar babu ita a gurin, ta san halin Aliyu sarai dan haka bata sake yunkurin sake yin wata maganar ba har suka isa bakin gate din gidasu. Bata jiran ya ce ta fita ta shiga gida, tasan halinsa farin sani ba tana da wahala ya iya bude baki yai magana musamman a inda zai iya isarda sakonsa da ido. Bude motar tai ta fita shi kuma ya hau titi ya dauki hanyar gidansa.

Horn daya yai aka bude mai gadin ya bude masa gate da sauri sanin cewar baya son jira, yayi minti biyar a cikin motar sannan ya fito yana rike da wayarsa ya nufi wata katuwar kofar mai ruwan zaiba. Door bell ya danna, Rahama ta bude masa kofa duk ta wani hade rai, kallonta yai from head to toe wani farin yadi ne a jikinta mai tsarin ja yadi ya fito da kyaunta da kuma dark skin dinta. Murmushi ya sakar mata kadan a maimakon ya fada mata cewar tayi kyau, sai ya ratsa gefenta ya shiga cikin falon kai tsaye sama ya haye ya shiga dakinsa dake cike da kamshin turare.

 

“Ni fa ba zan iya ba, na fada maka na gaji gaji”

 

Rahama ta fada bayan ta turo kofar dakinsa ta shigo, zuwa tai kusa da shi ta tana da yi masa mitar data saba.

 

“Aliyu na fada maka ni gaji, ga zafi sokoto ga wannan uban aikin fisabilillahi baka min adalci, baka tausayi na, tun farko sai da na fada maka ni ba zan iya zuwa na zauna ni kadai ba kace za a samu mafita gashi nan ka barni kullum sai sai wahala na ke ta yi”

 

Be dago ya kalleta ba, har ya gama cire agogon hannunsa ya bude maballan rigarsa sannan ya juyo ya rika kanta ya sumbanci goshinta ya saketa ya nufi bathroom. Ta saba inda fada ne zata yi ta gama be ce mata uffan ba wani lokacin ma har tambayar yake shikenan ko akwai wani? Magana tana masa wahala ainun kamar wanda aka idan yai maganar zata ragu .Haka rayuwarsa take tun yana karami indai ka girmeshi yai maka laifi sai dai kai ta nasa fada ka gaji ka bari ba zai ce uffan ba, idan kuma shi ne a sama da kai to baka isa ka daga kai ka kalleshi ba ma balle har kace zaka masa fada.

Baya son yanayi, magana tana masa wahala ko da zo ki karba ne, baya jira sai dai a jira shi, yawan kallo yana bata masa rai ko da kuwa shi zai shafe sa a daya yana kallonka ne, baya son hayaniya and when ever he say no that’s means no for sure. Duk wanda yake masa da shi a cikin familynsu tun daga dangin uwa har na uba babu wanda ya isa ya tsare Aliyu da kallo balle kuma har ya cilasta shi yin wani abu. Mommy ce kawai ta isa da shi sai Daddy bayan su babu mai kallon idonsa kai tsaye yai masa umarni da yi ko hani.

 

Wanka yai ya fito daure ya tawul fuskarsa kamar ko yaushe ma’ana babu far’a balle murmushi. Kamar be san da zaman Rahama a dakin ba haka yabi ta gabanta ya wuce zuwa gaban maduba yana shafe jikinsa da karamin tawul. Tsadadden man shafi mai kamshin gaske ya shafawa kansa sannan ya juyo ya nufi wani bangare na daki da aka ware aka zuba masa tufafinsa a ciki. Rahama ta biyoshi tana magana cikin bacin rai.

 

“Ni fa na fada maka na gaji”

 

Be ce uffan ba, kuma be bar mata wata alama da ke nuna cewar yaji abunda take fada ba, ba kuma dan be ji ba sai dan haka dabi’arsa. A gabanta ya kwance tawul din jikinsa ya shirya cikin wasu kananan kaya wadanda suka kara fitar da kyaunsa da kuma aibarsa fuskarsa sai annuri take kamar sabon ango. Wata yar karamar dorowa ya janyo ya dauko pen da memo aurensu yai rubutu a kai ya mika mata sannan ya fice daga gurin zuwa bedroom.

 

“Na yi Magana da Mommy tace za a samo aikin, amman tace ki daina wahala da yawa saboda ciwonki kuma Jawahir zata rika zuwa tana rika miki aikin gida”

 

Tana gama karantawa ta saki paper a nan, ta saba karanta abunda baya iya fada mata idan an maganar basa kusa, wani lokacin kuma sai ya zauna ha fada mata kamar ba shi ba. Yana gaban madubi yana fesa turare ya hangota ta fito sai ta jingina da kofar closet din tsa dayan hannunta ta rike kanta, da sauri ya aje turaren ya nufi inda take hankalinsa a tashe ya rikata ya dawo da ita jikinsa daga jikin kofar closet din.

 

“Kin cika yawan magana Dear, kuma kinsan matsalarki”

 

Ya fada yana kissing front head dinta.

 

“Na yi magana da Doc Asim yace za a samo very soon, idan an samu sai muje waje a dasa miki, i can’t wait to see you alive healthy”

 

Ya rumgume tsantsan a kirjinsa yana shafa bayanta kamar ba shi ba.

 

 

 

ATAA POV.

 

Sai da na kalleshi da kyau sai na gano ba shi yake min maganar ba, wata ce mace ce mai kama da shi take maganar   tare da ziro min hannunta mai kunshin lallen hausa wanda yai baki sosai a farin hannunta. Ba tsaya karbar kudin wankin motar ba domin gaba daya hankalina ya gama tashi sai na juya da sauri na koma can gefen titi na tsaya ina kallonsu, jira nake naga ko zai fito ya biyo ni amman sai naga be ko kalli inda nake ba, yarinyar ce kawai ki aiko min da sakon zagin da hannunta. Wutar traffic ta saki suka kama hanya shi da sauran mutanen da ke tsaye da motocinsu, sannan na soma tambayar kaina, wai wayar waya na sata? Yaushe nai satar? A ina nai satar? Na san muna da talauci da yunwa amman hakan be tana saka mu maida abun wani namu ba, yo ni ina ma naga wayar balle na dauka. Wata kila wata mai kama da ni ce tai satar to amman wayar waye aka sace a cikinsu? Ita ko shi? Idan tashi ce ai da shi zai yi magana ba ita ba, ita kuma ai ban tana ganinta ba balle har tace na mata sata ko dai shine yai min kazafi yace na masa satar?

Koma dai mienene zan yi iya kokarin da zan yi na ga ban sake ganin wannan hadaddiyar fuskar tasa ba, wacce bata ko kallon mutane da kima balle har ta martabasu, yau kwana uku kenan kullum idan na hadu dashi sai wani abu marar kyau ya faru da ni, da farko fitsari nai kuma ya watsa min ruwan kazanta, na biyu kuma kuka nai har da wani jefar da rigar dana taba shi sai ka ce ni din ba mutum ba ce, wannan karon kuma an laka min satar wayar da ban san kalar ba.

Har nai na gama na nufo hanyar gida babu abunda nake sai miti da surutun rashin alherin da yake tare da wacan mutumen iyakar alkawarin da na daukarwa kaina ba zan sake hadu da shi ba, da alama nan gaba cewa zai yi wani na kashe ko kuma ya takani da mota ya wuce.

Yau kam ban dawo da wuri ba, domin a hanya magariba tai min, hango manyan motoci guda biyu a gidan da zan iya kiransa da hamu yasa ni hanzarin cira kafa na karasa ciki da sauri, Nana na samu risine a kasa tana rokon wani mutum kamar zata fasa kuka.

 

“Dan Allah ke yi hakuri Wallahi babu inda zai je, shiyasa ya laba nan shi da yaranshi”

 

Babban mutumen mai rigar arkin dake nuna isarsa da tarin dukiyarsa ta dakawa Nana tsawar da har sai da naji ciki raina.

 

“Babu ruwana da wannan, akan mi za ku zo ku bata min gida, ku san nawa na zuba na siye filin nan, an fara min gini sai kawai ku zo ki shige kuna lalata min guri”

 

A nan nima na zubar da kayana na shiga rokonsa kamar yadda Nana ta hade hannayenta tana rokonsa.

 

“Baba dan Allah kai hakuri Wallahi idan ka koreni daga nan ban san inda zamu je ba ba mu da kowa”

 

“Ba ku da kowa daga sama kuka fado? Daga ina kuka taso kuka dawo nan? Ku koma can ni bana son ganinku anan, ku bar min gida na fada muku idan na sake zuwa na tarar da ku a nan sai na wulakanta ku”

 

Yana fadar hakan ya bude motarsa ya shiga, sauran mutane da suke tare da shi suka shiga dayar motar suka bi bayansa. Kallon mahaifiya dake kuka nai ina kwalla sai kuma na daga kai na kalli yar bukkarmu, miye laifin mu dan mun raba a wannan gidan tunda ba a ciki muka zauna ba, miye laifin bukkarmu mu dan kawai mun zauna a ciki.

 

“Yau ko mun shiga uku an koro mu can nan kuma an kore mu, yau ina za mu?”

 

Shine abunda mahaifiyata take fada ya yaren buzanci tana kuka. Zuciyata ta sosu sosai tana da gaskiya domin idan har kuma bar nan ban san wani guri da zamu iya rabawa ba, domin ba mu san wani gurin da zamu iya zuwa mu nemi taimakon gurin zama ba. Daga ni har Nana haka muka wuni cikin damuwa da rashin walwala har garin Allah ya waye, da safe Nana ta aika Lukman ya siyo mana waina ni da shi ita kuma ta gagara cin komai. Sai dai hakan be hanata fita bara ba, ni ce dai ban je ba, daman yau bana jin fitar saboda abunda ya faru jiya na laka min sata da kuma zancen barin gurin da muka raba, sai duk haka yasa ni jin kamar ma bani da lafiya, sai dai yau na samu yin sallah biyu a cikin lokaci tun a gida na wuni kuma bana aikin komai,  wato azahar da la’asar ban da Asuba da da nai bayan rana ta gama bayyana.

 

Can da yamma Nana ta dawo har da biredinta a hannu, Lukman na bayanta da gorar ruwansa rataye a wuyansa. Biredin kawai muka ci muka sha ruwa sannan ya dauko kudin da ta zo da su da sauran kudin da suke rage mana idan mun siye abinci gaba daya kudin ba su wuce dubu uku da yan kai ba.

 

“Wadannan kudi ba zasu iya mu kama haya ba, ni ban san yadda za mu yi ba”

 

Magana take ina karantar tashin hankalin dake zuciyarta har yake bayyana kansa a fuskarta, ni dai na yi shiru ina ta tunanin sama mana mafita.

 

“Nana ko mu nemi gadi wani gida? Ta yadda zamu samu gurin zama”

 

“Wa zai ba mace gadi? Idan mu mun samu ni ina zan iya tare barawo?”

 

“Ai dan mu samu gurin zama ne”

 

“Hakan ba zai yi ba, sai dai na bincika wani gurin ko Allah zai sa mu samu”

 

Tun daga ranar kullum Nana cikin neman gurin da zamu koma mu raba take amman ba mu samu ba, yawancin inda muke samu duka filaye ne mu kuma muna tsoron zama a fili sai dai a kangon gidan da aka fara aka bari ko kuma ba a karasa ba ko ya kuma ginin daya soma zubewa.

A kullum da fargabar zuwan Alhajin muke kwana mu tashi muna ta zuba ido ko zai zo amman shiru be sake zuwa ba har aka kwashe kwana kusan goma shabiyar, hakan yasa muka koma muna rayuwarmu ta yau da gobe cikin kwanciyar hankali. Musamman ni da ban sake saka wannan bakin mutumen a idona na ba. Yau ma da gari muka karya duk kuwa da kasancewar bana sonsa amman babu yadda na iya dole na ci ko babu dadi, bayan mun gama sha ne na tashi nai alwalar isha’i na kabbatar sallah. Ina cikin sallah na ji ihun Nana waccw ta kewa a bandaki kasa karasa sallar nai jin ihun yayi yawa na dauki fitilar hannu dake dakin na fito waje da sauri ni da Lukman muka nufi kewan ina Haskawa sai na hango katon maciji ya nade gurin daya yana ta zuro mana kansa, Nana kuma ta fadi gefe daya tana ta murje murje da alama cizonta yai ko kuma sara, Lukman ya saka kara ni kuma na saki fitilar a firgice na ruga izuwa titi cikin hudun hangon gidan ina neman masu taimaka mana, daman na san ba za a rasa irin wadannan abubuwan ba a guri kamar wannan, musamman da dare ba hudu yake zageyemu har sai idan mun kunna kara ko fita ko kuma hasken farin wata, wutar nepa kan sai dai mu hangota a manyan gidaje. Da ihu da karaji na isa titin gawon nama ina ta neman wadanda zasu taimaka mana, mazan da suke zama a gurin titi suka yo kaina da sauri ni kuma na shiga gaba ina gudu suna gudu har muka dawo cikin kangon gidan dake cike da hudu, masu wayoyi suka kunna wayarsu suka haske bandakin sai Nana aka gani babu macijin babu labarinsa, motsin kirki ma bata iya yi da sauri wani yace a bashi kyale sai ya daure inda yake zaton macijin ya tsareta wato kafar data rike.

 

“Ku nemo Napep? A kaita asibiti”

 

Daya daga cikinsu ya fada ni da Lukam babu abunda muke sai kuka ni ina rike da ita Lukman kuma yana tsaye bayana, a gurin wasu samarin ke kallo domin yau babu wannan bakin gentleman n a fuskata mai hana kowa ganin ainahin kyawo na. Ban san wanda ya kira Napep din ba nadai ga an shigo da ita har gurin Bukkarmu samarin suka rikata suka sakata ciki ni Lukman na shiga gaba ni kuma na zauna baya tare da ita ina hawaye kamar ba gobe.

Ko wane motsi nata jinsa nake cikin kashina ji nake kamar ciwon a jikina yake, mahaifiyata ita ce duniyata, na gwada kokarina akan tsagaita kukana sai na gano ashe ni ba ba Jaruma ba ce a gafen dauri. Wata asibitin kudi mai zaman kanta Mai Napep din ya kaimu a lokacin da muka isa emergency sai suka karbe mu da gaggawa aka wuce da ita ciki Mai Napep ya juya yai tafiyarsa ni da Lukman sai muka yi tsaye waje. Har sai da Nurse din ta dawo kirana ta dauki sunan Nana ta bukaci naje wani guri na karbo kati sai na tuna da babu sisi a tare da ni, adole na bar Lukman a gurin na fita na hau achaba na je na dauko kudinta gaba daya na dawo naje na biya kudin katin sai kuma aka ce likita na son ganina. Da sauri na nufi inda Nurse din ta nuna na tura kofar office din na shiga hankalina a tashe fuskata duk hawaye ya bata ta, hannuna rike da yar jakar da Nana take zuwa da ita bara wacce kudin suke ciki.

 

“Nurse tace kana son ganina”

 

“Ke ce wa?”

 

Likitan ya tambayata yana min wani kallo daga sama zuwa kasa, duk wanda ya kalli sutura baya bukatar na fada masa cewar ba mu da shi, tufafin da nake saye da su kawai sun isa su isarda sakon talaucin da muke tare da shi.

 

“Mamata na kawo wacce maciji ya tsara”

 

“ina Babanku?”

 

“Babanmu ya rasu”

 

“To ina yan’uwanku da ke zan yi Magana”

 

“Ko minene likita ka Fada min mamata bata da kowa a nan sai ni, duka yan’uwan mu suna nijar”

 

Na Fada idona na sake cika da kwalla. Kallo yai sai ya sake kallona sannan yace.

 

“Okay wannan allurar za ki siyo naira dubu ashirin da daya za ki kashe”

 

Ya Fada yana mika min wata farar takarda. Ina karba na juya jiki ba kwari zan fice sai na ji ya ce.

 

“Kina da kudin ne? Idan ba ki kawo maganin nan da wasu hours ba Mamaki zata iya mutuwa”

 

Juyowa nai idona na zubar da kwalla ma girgiza masa kai dan bana ko iya magana.

 

“Babu?”

 

Na gyada masa kai.

 

“Bude baki kiyi magana wannan asibiti na ce zan iya taimaka miki idan baki da su”

 

“Wallahi ba ni da su ban san inda zan samo ba, bara mu muke kamin mu saye abincin”

 

Shiru yai kamar mai nazari, sannan ya kalleni ya ce.

 

“Shikenan zan mata allurar kuma zan ya mata tiyata na cire dafin macijin”

 

Da sauri na risina kasa ina masa godiya wani irin jindadi ya rufe jin za a ceci mahaifiyata sai dai ban taba jin inda akai wa wani tiyata aka cire dafin maciji ba sai dai allura.

 

“Taso muje ki saka hannu a file”

 

Da sauri na mike tsaye ina share hawayena, yana gaba ina binsa har muka shiga wani daki mai cike da nurse da yawa ya dauko wata takardar ya miko tare da nuna min inda zan saka hannu. Hannunsa ya dora saman nawa yana yimin sigh din yadda zan hi daidai, ina daho kaina nai arba da wata nurse tana girgiza min kai alamar kai, sai dai ban gane abunda take nufi ba na tausayi ne ko kuwa na kar nai yi ne oho ni dai fatana a ceto mahaifiyata….

https://my.w.tt/GuQH5GZKb9

 

*Z A K I*

 

By Khadeeja Candy

 

 

4️⃣

 

Misalin goma aka shigo da ita tiyata amman basu fito ba sai karfe uku da wani abu na dare.

Anyi mata tiyata cikin nasarar Allah da iyawarsa, saidai a halin da naga mahaifiyata sai na kara matso da maraicin mu kusa ni da Lukman. A wani dakin mai kyau aka ajeta kamar matar wani babban mutum ko kuma wata hajiya, a jikinta an manna mata wasu na’urori har a hancinta a wani abu mai kamar kwanfuwuta nake kallon tafiyar numfashinta, sai dai tana kwance a gurin kamar gawa jikinta babu tufafi sai wani zanen asibiti da aka saka a lulluba mata.

Ina tare da ita har asuba ban runtsa ba, gani nake kamar zata iya farkowa ta bukuci wani abun ko da yake babu komai a tare da ni wanda zata iya ci ko ta sha, lukman ne kawai ke ta bachinsa hankalinsa kwance.

Misalin takwas da rabi likitan ya shigo cikin shiga ta kananan kaya da rigar likitoci a samansu fuskarsa a sake yana ta min murmushi kamar mun saba.

 

“Ina kwana?”

 

Na gaisheshi cikin girmamawa. Sai ya amsa min kamar be gane ni ba, ba kuma kallon rashin ganewar bane, wata kila sai a yau ne yake tantance irin hallittar da Allah yai ta kyau mai daukar hankalin mace balle kuma namiji.

 

“Miye sunanki?”

 

“Aisha amman ana kirana Ataa”

 

“A nan kuka kwana?”

 

Ya tambaya yana kara tantance kyawun surar jikina.

 

“Eh”

 

“Ayyah ban sani ba ai da na kawo muku abun shimfida ko kina da shi”

 

Na girgiza kai alamar aa a cikin yanayin dake nuna dukan hankalina da damuwata tana gurin mahaifiyata ne.

 

“Da gaske baki da kowa a nan Nigeria? Ku yan nijar ba naga akwai wadanda suke da yan’uwa a nan ba?”

 

“Ni ba mu da su, ba a mu da kowa a nan”

 

Na fada masa cike da gundira da tambayoyinsa. Sai naga yayi murmushi kamar wanda jin hakan yai masa dadi, sai ya saka hannunsa aljihu ya nufi mahaifiyata yana dubata.

 

“Ki samo riga ki saka mata da zanen da zai iya rufe kafafunta, na bada a siyo mata maganin dubu dari da bakwai manyan magunguna ne masu tsada yadda mahaifiyarki za tai saurin jin sauki kuma an mata allurar bayan na mata sai nai mata operation na cire mata dafin macijin”

 

Wani irin dadi ne ya lullube ni sai na rasa ta inda zan fara masa godiya, hawayen farinciki suka cika ido har naji kamar na dauke shi na hade, a rayuwata ta duniya tunda Nana ta haife ni ban taba karo ko ganin mutum mai tausayi da jinkan masarasa irinmu ba kamar wannan likitan.

 

“Na gode Allah ya biyaka ya saka mata da alheri, Allah ya daukaka asibitinku Ya saka maka da aljanna ka taimaki rayuwata sosai ba zan taba manta ka ba”

 

Murmushi yai yasa hannunsa aljihu ya ciro kudin da za su kai dubu goma ya miko min.

 

“Ga wannan, ki je ki siya abinci ki yi duk abunda kike bukata, kuma idan mahaifiyarki ta farka ki kirani karki bata komai”

 

Wannan karon addu’ar gamawa da duniya nai masa, domin a tunani ita kan aljannah da duniyar duka ya sameta, domin mutum mai taimako mai share hawayen masara shi Allah yai masa alkawarin aljanna kamar yadda Annabi yace shi da mai taimakon maraya kafada da kafada za su shiga aljanna da shi. Babu abunda nake hangowa sai matarsa tabbas tayi dacen miji domin samun miji mai taimakawa al’umma har su yi masa addu’a ta yi babban dace.

Bayan ya fice ne na kama hannun Lukman muka fita zuwa gida, sai dai abunda na tarar a gidan sai yafi tada hankalina fiye da ciwon mahaifiyata. Yar bukkarmu ce aka hankade can gefe aka cire kwannon da maihaifiyata ta saka domin zagaya yin fitsari ko ba haya, kayan abincinmu da tufafinmu an watsar da su can gefe gaba daya an watsar da komai. Tsaye nai ina kallon yadda kayan idona cike da kwalla, ba komai yasa ake mana haka ba sai rashin, rashi kuma na kudi saboda talaucin da yake tare da mu da kuma rashin kowa a kusa da mu. Lallai muhalli babban abu ne, da ace haya muke ko mallakinmu ne da wani be isa ya wulakanta haka ba saboda kawai mun raba a gidansa dan mu zauna.

 

“Ataa waya maka mana?”

 

Lukman ya tambaya yana bata fuska kamar zai yi kuka, ban da jansa jikina na rumgume babu abunda nai domin ina jin idan har na bude baki nai masa magana kuke kawai zai fito domin shine cike a zuciyata. Waiga nai banga kowa ba, da alama ba aikin yau ba ne idan kuma har yau akai shi tabbas tun da farar safiya aka zo aka mana haka aka tafi. Bani da wani zafi daya wuce na share hawayena na shiga hada tarkacen mu ni da Lukman babu inda zan kaisu gashi ni kuma ban iya hada bukkar ba balle na sake yin wata, Nana ce ta iya hadawa ita kuma tana asibiti, ance zuciyata tana ga mai kudi idan aka masa abu sau daya ba za akara ba, domin zai dauki mataki wanda bashi da shi kuwa sai ayi ta maimata masa kuma ya shanye yai hakuri saboda bashi da shi, ganin babu inda zan kai kayan yasa na hada komai na je can cikin wani daki da yake a kangon gidan da ba a karasa ba na saka su ni da Lukman sannan na fito waje na samo duwatsu na hada murhu na dauki jaran bukkarmu na saka na aiki Lukaman ya siyo mana ashana da taliya da cefanen dafa taliyar. Ni kuma na wanke tukunyar da mike girki da ita sannan na gyara tarugu da albasa na nufi gidansu kawata Farida dan na jajjaga, da nai sallama mahaifiyarta na ji taki ta amsa min a zatonta rokin wani abun na zo kasancewar wani lokacin idan ba mu da ashana ko gishiri tana aikawa tace ta sammata, har take yawan cewa wai mun cika roko, ni ko a ganina duk wanda zai mika maka hannu yace ka bashi tabbatas oa fishi kuma dan kana da shi ne ake zuwa nema a gareka amman mutane da yawa ba su fahimci hakan ba. Sai da na karasa har bakin kofarta ina sallamar sannan ta amsa min na gaisheta ta amsa ciki ciki.

 

“Dan Allah turminku za ara min zan jajjaga tarugu ne”

 

A tsaye ta bar ni a gurin na kusan minti biyar tana ta kallon arewa 24 a karamin tv ta sannan ta dago ta kalleni.

 

“Gashi can gidan kin gama ki dauraye”

 

Ta fada min a cikin yanayin da ke nuna alamar bata son ara min kamar yadda take yawan yi min idan na zo nema abu, shiyasa bana son zuwa idan ba Farida ce a gidan ba ita ce mai min maraba wani lokacin har ta tayani dakawa duk kuwa da irin fadan da mahaifiyarta take mata na kin jinin abotarmu da take. Ni kuma babu wani gida da zan iya zuwa na roki abu kamar irin gishiri ruwa ko ashana ko daka wani abu kamar wannan gidan, domin duka gidanjen da suke kewaye da mu na manyan mutane ne, a ina zan iya shiga roko ayi min kallo banza wani gidan ma ko gate din su ka taba sai mai gadin yace maka basa nan saboda kawai anga yanayinka na masu bukata ne.

Daf da zan gama jajjagen ne take tambaya wai ance maciji ya tsari mahaifiyata, ni kuma na amsa mata na kuma bata labarin yadda abun ya faru har ma da taimakon da aka mana a asibiti, sannan na kwashe jajjagen na wanke mata turminta kamar yadda ta bukata na yi mata godiya na juyo na fito.

Hura wutar na fara yi na dora tukunyar na zuba mai da sauran abubuwa a take saboda tsananin yunwar da nake ji, haka nai ta bankawa girkin wuta har ya dafu na zubawa Nana a wani kwanon mai murfi Lukman kuma na saka masa a nasa kwano na zubawa kaina, na kwashe saura a wani kwanon na rufe, sai na zauna na tisa abincin a gaba na kasa ci babu komai a zuciyata sai kewar mahaifiyata da tunanin ruguje mana bukka da akai, a take na nemi yunwar na rasa, kuka ya maye min gurbinta har sai da Lukman din ma ya fashe da kuka ganin yadda nake ta kuka. Abincin na aje na shiga ciki na daukowa Nana riga da zane na saka a jakar da kudin suke ciki na jira Lukman ya gama cin abinci ya wanke hannunsa sannan na dauki abincin Nana muka fito bakin titi na tari Napep muka shiga ni da shi muka doshi asibitin.

 

 

 

 

ALIYU POV.

 

Bachi Rahama take ta yi tun bayan sallah asuba har goma ta gota, a saman wani katon gado mai tsada da katifa mai kyau take kwance, ta lulluba da blanket mai laushi kamar kada, ta saba da hutu da jindadi haka take bachi har sai ta gaji dan kanta ta farka.

A lokacin Aliyu na falo zaune saman wata lallausar kujera rike da kofin tea laptop a saman ciyoyinsa yana duba yanayin yadda aikin gas din kamfaninsu na Abuja yake tafiya. Sanye yake da short jean da farar vest, a gabansa wani katon tv ne mai dauki da farar baturiya tana watso labarai a channel din Al Jazeera. Wayar ce dake silent tai haske sai dai be lura ba, domin ya cire ringing din, baya so hayaniya ko kadan that’s why he choose Abuja a gurin aikinsa to because its a quiet place for him, ko da wani meeting din ne ya taso wanda yasan za a iya hayaniya da cece kuce sai ya tura abokinsa Umar. Be lura da kiran ba har sai da ya gama abunda zai yi ya juya da zimmar aje laptop din sai ya hango wayarsa tana haske, hannu ya kai ya dauki wayar ganin Doc Asim yasa shi sauri picking.

 

“Hello Doc”

 

“Ranka ya dade ina ta kira baka dauka ba”

 

“Yeah ina wani aikin ne, sai yanzu na lura”

 

“Na kira na maka albishir ne cewar an samu Kidney din”

 

Kofin tea dake hannunsa ya aje ya mike tsaye da sauri cike da farinciki marar misaltuwa har ya saka shi kin yarda da maganar da Doc ya fara masa sai da ya sake tambaya duk kuwa da yasan be taba masa karya ba.

 

“Doc are you serious?”

 

“Wallahi da gaske nake, gani nan ma gurin Alhaji abunda muke tattaunawa kenan”

 

“Wow gani nan zuwa”

 

Yai saurin waje wayar ya nufi bedroom dinsa cike da farinciki, labulayen dake fuskarta gadon ya bude sai ga hasken rana yana haske gadon kasancewar gaba daya gaban dakin glass ne. Jin hasken rana yasa ta lunkumewa cikin blanket tana bata fuska, sai ya zauna bakin gadon ya yaye blanket din ya dagota.

 

“Dear wake up yau ranar farinciki ce”

 

“Ba yau na ke birthday ba sai next month”

 

Ta fada ba tare data bude idon ba.

 

“Ba maganar birthday za ki yi birthday cikin koshin lafiya In-Sha-Allah, Doc Asim ya kirani ya fada min yana gurin Daddy suna tattaunawa an samu Kidney din”

 

Ba idonta kadai ta bude ba har da baki da da hancinta duk a bude suke jin wannan daddan labarin, da sauri ta kama hannayensa.

 

“Dear da gaske”

 

Ya gyada mata kai yana kallonta da cat eyes dinshi sai ta rungume shi da sauri ta fashe da kukan dadi. Dan murmushi yai kadan ya shafa bayanta.

 

“Congratulations Dear you save me”

 

“I said i would”

 

Ya fada yana dagota daga kirjinsa yana share mata hawayenta.

 

“Tashi ki shirya zan kaiki gidanku ni kuma na wuce gurin Daddy na gana da likitan naji yadda za ayi”

 

“I love you”

 

Ta fada tana kuka, sannan ta daga daga jikinsa ta sauka ta shiga bathroom ta sauka cikin kankanen lokaci ta fito shima ya shiga yai ko daya fito har ta shirya, shima be dade gurin shiryawa ba dan ya matsu ya hadu da likitan.

 

“Idan munje can zaki karya promise?”

 

“Promise”

 

Ta fada tana saka bakinta cikin nashi, musanyar yawu sukai halshenta da nashi suka hada auratayya sannan ta sake shi ya rika hannunta suka fito tare. A tare suka sauko kasa hawayen farinciki tana cika idonta, har ya bude mata motar ta shiga sannan ya zagaya ya shiga ya yai mata key tun kamin yai horn mai gadin ya bude masa gate suka kama hanya gidan Alhaji Nasiru Gobir.

Cikin kankanen lokaci suka isa gidan nan ma horn daya yai aka bude masa gate, tun kamin yai parking Rahama ta bude motar ta fita ta shiga cikin gidansu da sauri, shi kan sai da ya faka motar sannan ya fito ya rufa mata baya. A falo ya sameta tana zaune kusa da mahaifinta.

 

“Daddy naga kamar kana cikin bacin rai”

 

“Wallahi wasu wulakantaccin mutane suka shige min a gidan da nake ginawa a Clapperto road, ance sun janyo har macizai suna shiga gidan, amman na ce a korasu”

 

Hannunsa ta kama.

 

“Daddy kar wannan ya dame ka yau rabar murna ce na Doc Asim ya kira wai an samu kidney din”

 

“What”

 

Gaba daya suka amsa har kanenenta suka taso ta sauri suka rumgume ta suna ta murna. Alhaji Nasiru ya kalli Aliyu irin kallon ganin kima da kauna ta suruki da surukinsa.

 

“Mun gode sosai Aliyu Allah ya saka da alheri”

 

“Karka damu Alhaji aikina samawa Mamata lafiya ko ta hali yaya, zanje gida san na samu ganawa da likitan”

 

Daga haka yai musu sallama ya fito ya shiga motarsa ya dauki hanyar family dinsu wato gidan Alhaji Garba Fayau…

 

 

 

_________________

 

Wayyo Ataa 😪

https://chat.whatsapp.com/DaDP34cM3s5FMfaQOtFM9Y

 

*Z A K I*

 

By Khadeeja Candy

 

 

5️⃣

 

Ko da mu ka isa asibitin ana ta mopping ko’ina, ni da Lukman muka rakube kamar sauran talakawa irinmu, wadanda suka tsaya suna jira a gama mopping din sannan mu wuce, masu hannu da shuni kan da masu galihu wucewa kawai suke ba tare da n tsayar da su ba, masu aikin sai mika musu gaisuwa suke.

Mu kam mu kai tsaye har aka gama mopping din sannan na mika kafata na taka sai wata daga cikin Nurses din da suke tsaye a can babban kofar shiga ta daka min tsawa data saka hantar ciki ta kaďawa.

 

“Ke ki ka fi kowa a nan ne da za ki tsallako ki wuce gurin be gama bushewa ba”

 

Da sauri na koma baya na tsaya gurin da na ke tsaye dazu, sosai tsawar nurse din ta firgita, da alama idan na sake taka gurin zuwa za tai ta mareni. Ina rike da hannun Lukman da jakar dana sakawa Nana tufafin dana dauko mata, Lukman kuma na rike da taliyar da ke cikin kula mai murfi dabam kular ma dabam. A haka muka tsaya a gurin kamar wasu marayu har gurin ya gama bushewa, da na ga wasu sun fara takawa sannan muka taka muka doshi ciki, sai kuma muka tarar dan cikin ward din be gama bushewa ba wani gurin ma a yanzu ne ake mopping din.

Dan Albarkar likitan nan yana tsaye da wasu nurses suna masa wani abu a takardu, yana hangomu ya ce mai mopping din ta tsaya mu wuce, cikin sauri ta tsaya muka fara takawa zuwa inda dakunan suke, wani dadi na ji ya lullubeni ko ba komai ya nuna min karamci da kulawa a matsayina na ba kowa ba, a take na ji kimarsa da darajarsa ta karu a idona. Sai da na gaisheshi sannan na wuce dakin da Nana take ciki, nurse din nan ta jiya na tarar wacce ta ce rika girgiza min kai lokacin da zan saka hannu a takardun da aka yi wa Nana aiki.

 

“Ina kwana?”

 

Na gaisheta cikina cike da tsoro gani nake kamar ita tsawar zata daka min kamar waccan nurse din. Sai na ga ta amsa min da lalama tana min kallon tausayi.

 

“Lafiya kalau, wannan matar mamarki ce”

 

“Eh mamata ce”

 

“Ina Babanki ya ke?”

 

“Baba na rasu?”

 

“To waya kawo ta asibiti?”

 

“Ni na kawo ta”

 

“Ba ku da kowa nan ne?”

 

Na dan yi shiru ina nazarin irin tambayoyin da take min da suka yi kama da wadanda likitan can yai min dazu, ban san dalilin da ya saka suke son yi min irin wadannan tambayoyin ba. Har na bude ba ki na bata amsa sai ga likitan nan ya turo kofa ya shigo yana waya baki har kunne sai dariya yake, sai dai ganina da wannan nurse din yasa yai hanzari katse wayar ya hade fuska kamar be taba dariya ba.

 

“Me kike a nan?”

 

Sai nurse din ta sha jinin jikinta ko motsin kirki bata yi.

 

“Na na na… Zo duba… Ta..”

 

“Ke duba ta ke kika aje ta? How dare you? Fita ki ba ni guri”

 

Kamar zata 6ace 6at a gurin haka tai saurin ficewa jikinta sai rawa yake kamar mazari, a nan nima na shafawa kaina lafiya fahimtar cewa yana da fada sosai na koma gafe ni da Lukman muna kallonsa. Yana kallona sai ya sake fuskarsa yai min murmushi yana kallon jakar hannuna.

 

“Miye a ciki?”

 

“Kudin da ka ba mu ne, da tufafin da ka ce a daukowa Nana”

 

Na amsa cikin tsantsar ladabi da kuma muryar da ke nuna babu ruwana.

 

“Wannan fa”

 

Ya sakw tambaya yana kallon kular da ke hannun Lukman.

 

“Taliyar da na dafa ce na kawo ma Nana ko za ta ci”

 

Dariya yai yana kallon murfin kular da ke daban da kular wacce ta soma koredewa wani 6angare na jikinta ma har ya tsage.

 

“Ya ma sunanki?”

 

“Ataa”

 

“Ataa karki sake kawo abinci a nan asibiti, zan sa a rika kawo muku na safe da na rana da kuma na dare ke da kanenki da kuma Mahaifiyarku idan ta farko kinji?”

 

“Da gaske?”

 

Na fada ina kara girmama kirmarsa lallai a cikin dubu samun mutum kamar wannan likitan mai tausayi da taimako sai an tona.

 

“Yes”

 

Har kasa na kai idona cike da hawaye ina masa godiya kamin na koma yi ma Allah godiya daya hada mu da irin wannan mutumen. Karasa yai ya duba Nana ya canja mata wasu abubuwan na na’ura sannan ya juyo ya kalleni.

 

“Ina tufafin suke?”

 

“Ga su”

 

Na mika masa da sauri a zatona saka mata zai yi sai naga yai baya da sauri kamar mai kyama.

 

“No no bari na kira wata ta saka mata”

 

Daga haka ya juya ya fice, ni kuma na kuma kusa da ita na tsaya ina ta kallon fuskarta ga ta a kwance kamar ta mutu, amman fuskarta na kyalli kamar zata bude baki tai mana magana.

 

“Ataa yaushe Nana zata tashi?”

 

Lukman ya tambaye ni yana kallonta.

 

“Ni ma ban sani ba”

 

Na amsa masa idona taf da hawaye tausayin mahaifiyata ya cika zuciyata, na san Allah ne ya kaddaro mata haka amman macijin nan be kyauta min ba. Ina tsaye wata mata mai zubin marasa mutuncin ta turo kofar ta shigo fuskarta ta tsage tana sanye da uniform din nurse sai wani kallo take watsa mana a hankade.

 

“Ke kamar ki za ki ace ba ki iya sakawa mahaifiyarki riga?”

 

Ta fada tana fisgar rigar a hannuna sannan ya karasa gurin Nana, yadda ta saka hannu ta tallafota sai ta tsikar jikina ta tashi dan zaka rantse da Allah ka ce karamin yaro ta dauka, a gabana gaban Lukman ta janye mayafin da aka rufe Nana da shi ni da Lukman muka ganta tsirara haihuwar uwarta ga dinki a cikinta gurin yayi ja sosai kamar jini ya kwanta, da sauri ya juyar da fuskar Lukman ni ma na juya muka ba ta baya hawaye na sauko min, ban juyo ba sai da na tabbatar ta gama ta rufe mata zane har na watsa min wata magana marar dadi jin.

 

“Tufafin ma duk ďoyi suke yi mtswwwww”

 

Ni dai ban ce mata komai ba na karasa gaban Nana ina kallon yadda yake ya mutsa fuska duk da kasancewar bachi take ko kuma ma na kira shi da suma, da alama taji zafin yadda nurse din ta motsa ta, ji nai kamar ace ina da wata dama da zan bawa ciwon umarni ko kuma na saka hannu na dauke mata shi ta farka ta tashi mu bar asibitin nan, ga dukan alamu likitan nan ne kawai mai mutumci sauranka ko kallo ba mu ishe su ba. A kujerar da ke gaban gadon na zauna ni da Lukman sai ya kwanto jikina kamar wani maraye yana ta tabe baki alamar zai yi kuka, ni kan daman hawayen kawai na ke ina jin wani abu ya tsaya min a zuciyata.

Kamar yadda fada haka kuwa akai misalin uku saura na rana aka aiko mana da abinci irin na manyan restaurant mai dadi har da naman kaza, a take Lukman ya hau murna jikinsa har rawa yake ya dauki naman kazan ya kai baki, ni kan sai na ji bana son cin komai duk kuwa ni da irin kwadayina. A bandakin na shiga nai alwala nai shimfida dankwalina nai sallah azahar, babu komai a sujida ta sai rokon Allah ya bawa Nana lafiya.

 

 

ALIYU POV.

 

Yadda ya ke driving sai ka rantse da Allah ba jiransa ake ba, hankalinsa a kwance yake tukin motar yana tafiya kadan-kadan duk kuwa da irin son ganin Doc Asim da yake. A ka’ida ba ya danna horn sau biyu sau daya ya ke yi amman wannan karon sai da ya danna har sau uku sannan mai gadin ya bude masa gate, tsayawa yai dai-dai gurin mai gadin ya sauke gilashin motarsa yana watsa masa wani kallo na marasa ganin talaka da daraja ya ce.

 

“Kar ka yarda na sake danna horn har uku ba ka bude min gate ba”

 

“Ayi hakuri ranka ya dade, Wallahi na dan zagaya ne”

 

Dattijon mai gadin ya fada jikinsa na rawa.

 

“An aje ka nan ne dan ka zagaya?”

 

“Ina nufin bandaki na shiga”

 

“Kai ya shafa ni dai na fada maka next time korarka za’ayi”

 

“In-Sha-Allah hakan ba zai sake faruwa ba, ayi hakuri Zaki”

 

Uffan be sake ce masa ba ya faka motarsa a harabar gidan sannan ya fito yana ta kanshin turaren da ke sanar da zuwansa ya shiga falon. Khaleesat da Hauwa na zaune a falon ko wace rike da waya, ganinsa yasa sukai mugun shan jinin jikinsu suka natsu sosai ko kallon inda yake ba sa yi gudun kar ya su hada ido da shi ya ce sun masa ba dai-dai sun san shi sarai ya tsani kallo.

Ganin Momy da Daddynsa yasa ya saki fuska ya cire talkamin kafarsa ya karasa kusa da su da sallama. Dukansu fuskarsu dauke take da murmushi da alama suna cikin jindadi da farinciki.

 

“Dan wajen Fulani ka yi lattin zuwa likitan kuma ya ce yana da aiki da yawa a asibiti be tsaya jiranka ba ya tafi”

 

Momy ta fada tana kiransa da sunansa da ta saba kiransa.

 

“Ya ce min an samu kidney din”

 

Ya fada yana mikawa Daddy hannu su gaisa. Sai Daddy ya dora da

 

“An samu, na masa magana ya ce zai hada ku da wani likita da za ku je London ayi mata dashen”

 

“Samun Kidney ba abu ne mai sauki a yanzu ba, gaskiya likitan nan ya cancanci komai daga gurina, at long last Rahma zata samu lafiya”

 

“Ba daga gurinka ya cancanci komai daga garemu ma gaba daya, amman ina fatar ba ta wani ya cire ba, domin ba kowa zai yarda ya bada kodarsa ba”

 

Aliyu yai shiru kamar mai nazari can kuma ya kalli Mommy ya ce.

 

“Ba lallai ya zama haka ba, kin san Nigeria ce, akwai talakawan da ba su san darajar kansu ba, za su iya siyarwa saboda kudi”

 

“Amman ko talaka sai wanda talaucinsa ya kai makura gaskiya, ai sai da lafiyar ake neman kudi”

 

Momy ta fada with doubt. Aliyu yai murmushin kasaita.

 

“Momy kenan ba ki san talaka ba, na san Doc Asim zai iya siye zuciyar talaka da kudi ya samu abunda ya ke so, domin ya san shi ma zai fanshi fiye da haka a garemu, shi fa talaka wawan mutum ne, indai za ka nuna masa kudi to zai maka komai na duniyar nan”

 

“Wato ďan wajen Fulani kai da Maman ka Fulani ban san wanda ya fi wani kyamar talaka ba, su ma fa mutane kamar mu duka daya muke a gurin Allah”

 

Ya kalli Momy cike da mamakin yadda take hakikancewa idan ana maganar talaka.

 

“Momy kenan, ai Mama Fulani gaskiya ta ke fada, tsakanin mu da talaka sai dai akwai mu amfana da shi shi ma kuma ya amfana da mu ta hanyar biyansa hakkinsa, amman ni ko abota bana fatar ta hada ni da talaka”

 

Daddy yai murmushi yana dafa kafardar Aliyu ya mike tsaye.

 

“Sai ka yi hanzarin samun Doc Asim ku tattauna, kasan matsalar matarka ita dayar kodar na daf da daina aiki”

 

“Yeah haka za ayi, san same shi mu tattauna, Thank you Dad”

 

“Your Welcome”

 

Daddy ya fada yana nufar hanyar da zata sadashi da part dinsa. Momy kuma ta mike tsaye tana fadin.

 

“Talaka ba shi da kima a idonka kai da uwarka Fulani”

 

“To ai ba shi da kimar ne Momy ki ce kin ki gane sai hada shi kike da mu, bayan kuma ba daya ba ne, as long as ba da ganganci Doc Asim ya cire kidney din nan ba babu abunda zai dame ni, ni zalince ne kawai ba na so, indai na san na biya ka to dole ka min aiki ba wani uzuri da zan dauka, so indai siyenta Doc Asim yai ni ya kyauta min wlh kuma zan bashi fiye da abunda zai tambaya”

 

Ya fada yana mikewa tsaye ya nufi dinning area, wani kebantaccen guri ne da ya kusan ayi babban falo da shi amman ba a zuba komai a gurin ba sai kato dinning table da freezer, daya daga cikin kujerun dinning din yadi aja ya zauna yana kallon Momy wacce ta taso ta nufo shi tana fadin.

 

“Ba ka ci abinci ba ka fito? Matar ta ka har yau ba ta iya girkawa ta baka ba?”

 

“Momy kin san lafiya be isheta ba, kodar ďaya da ke jikinta ma ance ta fara lalacewa, so ba komai na ke bari tai ba, and Momy kin san wahala ai sai talaka”

 

“Au ni da nake shiryawa Daddynku fa?”

 

Murmushi yai kadan yana dora duka hannayensa saman dinning din.

 

“Ai ke Momy saboda kin kwana biyu ne, ke da kina da kurciya ai Daddy ba zai bari ki yi girki ba, i rather na yi oder a restaurant da nai forcing dinta ta girka min, besides ba komai ta iya girkawa ba ita a gidansu ba aiki take ba”

 

Momy ta tabe baki tana saka masa sikari kwaya biyu a kofin tea. Bayan ya gama karyawa ya sauko daga dan stairs din dinning din yana taba wayarsa ya nufi kofar fita kanensa na mika masa gaisuwa. Kai kawai ya daga musu ba tare da ya amsa musu ba sai kara hade fuska yake kar su ga damarsa.

Fitowa yai harabar gidan yana amsa kiran Rahma, da yai picking shiru yai har sai da ta fara magana cikin yanayin damuwa duk da irin faduwar da gabansa yai jin muryarta kamar tana cikin damuwa.

 

“Dear ina driving na kade wani”

 

“Hope babu abunda ya faru?”

 

“Ya ji mu a kafa da kai”

 

“Lafiyarki na ke tambaya”

 

Ya tambaya kamar maganar bata son fitowa daga bakinsa, sai dai tashin hankalin da ke zuciyarsa da burin jin lafiyar matarsa ya saka shi fidda numfashi kadan-kadan.

 

“I’m fine amman shi mutumen ya ji ciwo”

 

“As long as be mutu ba, ba wata damuwa ba ce, turo min address din inda kike yanzu”

 

Be jira abunda zata ce ba yai hanging, he don’t mind ya tambayi inda zata je ko abunda ta je yi, saboda ya yarda da matarsa ko kasar zata bari bata fada masa ba ba damuwarsa ba ce indai zata je kalau ta dawo kalau. In few minutes ta turo masa sakon inda take sai ya forward massage din to the one of his bodyguard.

 

_Ka samu Madam a wannan address din, ka biya wanda ta kade ko dubu nawa ya ke so, and make sure matata ta isa gida lafiya_

 

Yana tura masa sakon ya mayarda wayarsa aljihu ya nufi motarsa yana wani shan kamshi.

 

 

ATAA POV.

 

Hankalina ya tashi sosai lokacin da na ga yamma ta gabato mahaifiyata bata ko matsa ba balle ta bude ido, ban san kan aikin asibiti ba, amman a yadda na ke jin ana cewa ko tiyata akai wa mutum indai ya kwana ya wuni yana farkowa sai dai tawa uwar shiru. Ina ji ina gani yunwa ta saka ni a gaba tana ta cina ni kuma na gagara kai ko da ruwa a bakina na natsu ina ta sauraren kukan da cikina ya ke min. Shiru shiru babu wanda ya sake leko dakin likitan be dawo ba, sai da yasa an aiko mana da abinci dare, a nan Lukman kawai ya ci ni kasa ko da kallon abincin balle na kai hannu na ci.

Bayan na gama sallah isha’i ina ta kaiwa Allah kukana, sai na hango Nana na motsa har tana yawo da kanta, da sauri na mike na tsaye na rika gadonta ina kiranta cike da jindadi.

 

“Nana Nana Nana”

 

Shiru bata amsa min ba sai juya kan take yana dantsar baki kamar bata cikim hayyacinta, ban yi dabarar na je kiran nurse ba balle kuma likita sai kawai na daga zanen da aka rufa mata na ga inda aka mata dinki yana fitar da jini kadan-kadan  ganin hakan yasa na fita daga dakin da sauri na nufi wani dan guri mai kamar reception inda nurses da yawa maza da mata suke tsaye wasu kuma a zauna.

 

“Mama ta ta motsa amman bata magana kuma na ga jini gurin da aka mata aiki”

 

Na fada cike da damuwa, sai duk suka tsaya suna min wani kallo kamar na kyama, a nan na kalli tufafin jikina hakika na yi dauda sosai tufafin da ke jikina wadanda na saba sakawa ne kullum, kuma ba damuwa nai da na wanke ba, gashi dazu na ji girki da kara sun kara datti, sai dai ba da dauda na ke a yanzu ba ta lafiyar Nana na ke. Daya daga cikinsu taja tsaki kamin ta aje biron da ke hannunta ta nufo ni tana fadin.

 

“Ni Wallahi ba son irin kazaman patient din nan na ke ba, idan kuma ba ka kula su ba ace ba ka yi aikin ka ba”

 

Sai sauran suka saka dariya, sai duk na ji na muzanta na ji babu dadi amman hakan be hana ni binta a baya ba ita kuma tana gaba har muka shiga dakin.

https://chat.whatsapp.com/HlKVwXU1HwlIrs8jJeHHqZ

 

*Z A K I*

 

By Khadeeja Candy

 

 

6️⃣

 

ALIYU POV.

 

Kamar kullum idan zai kwanta sai ya tsaya ya duba wasu abubuwan a laptop dinsa haka ma idan ya tashi da safe musamman abubuwan kamfaninsu na samar da gas wato Sky Global Resources, babban kamfani ne da babu irinsa a nigeria wanda ke samar da gas da man fetur da ma hako wasu ma’adanai na kasa da saffara su, kuma shi yake wakiltar babban reshensu da ke Abuja inda ake tura komai, hakan yasa dole komai rashin lokacinsa dole ya matse a haka ya kula da wasu abubuwan.

A dakinsa ya ke amman ko’ina n dakin kanshin expensive perfume din Rahma yake, yana daf da rufe laptop din Rahma ta turo kofar dakinsa ta shigo hannunta rike da mug, bakinta ya sha janbaki har kyali yake, wata rigar bachi ce a jikinta mai kamar rariya, komai na jikinta a bayyane yake kamar ma bata saka ba komai ba. Dagowa yai yana kallon yadda ta nufo shi tana wani irin taku kamar kwararriyar karuwa, da fuskarka ta miskilanci, a lokacin da ta karaso kusa da shi sai ta kurba ginger tea dake cikin mug din a bakinta ta saka dayan hannunta ta dauke laptop din dake jikinsa ta aje gefen gadon da yake zaune ta raba kafafunta biyu ta hau saman cinyoyinsa ta juye masa tea a bakin. Murmushi yai bayan ya hade tea ta karbi mug din hannunta ya aje kan bedside drawer ya wutsilo da ita saman gadon ya zama na shi ne a samanta yana ta kallon bakinta wanda ya sha janbaki.

 

“Kin san lafiyar jikinki bata ishe ki ba, amman sai neman fitina, idan kuma na biye miki ciwon ki ta shi ko?”

 

Ya fada mata kadan kadan kamar mai rada yana ta yawo da cat eyes dinsa a fuskarta. Murmushi tai ta san halin Ali Zaki baya wasa da wannan bangaren komai fushin da yake ko damuwar da yake ciki, duk miskilancinsa da jin kansa indai ta wannan bangaren nan na da nan za’ayi saurin kama shi.

 

“Ina ta tunanin abunda zan yi na saka maka ne, Aliyu kana kokarin kawarda duk wani abu da zai taba ni, a sadakar a lokacin da likitan nan ya fada min cewar kidney ta daya ta samu matsala, bayan kuma an cire daya, na dauka mutuwa zan yi amman gashi yanzu za amin dashen wata na samu lafiya”

 

“Komai zan miki Dear, na yi magana da Doc Asim dazu da rana har ya hada ni da likitan da za muje UK tare da shi, In-Sha-Allah within week din nan za mu gama duk wani shirye-shiyen sai muje can a saka miki, i will pay Doc Asim a huge of money saboda wannan abun da yai min, zan yi masa godiyar saving a billionaire naira wife”

 

Ya fada yana kissing din wuyanta, tare da saka halshensa yana wasa da gurin.

 

“I promise you idan kika samu lafiya ba zan raga miki ba”

 

Ya fada sound so sexy kamin ya shiga aika mata da sakwanni masu zafi…….

 

 

 

ATAA POV.

 

Lokacin da nurse din ta shigo ta dubata sai ta kalle a hartsine ta ce.

 

“Farkawa ne za tai, kuma wannan jinin ai dole ya fito tunda jiya akai tiyatar be gama bushewa ba”

 

Nurse din ta fada kamin ta kalleni.

 

“Ga ki kyakkyawa kin maida kanki kazama”

 

Ko kadan ban kula wata maganarta ba, wani dadi na ji ya lullube ni jin cewar farkawa ne Nana za ta yi, sai raina ya fara fari, wani irin shauki ya kamani na ji kamar na taba ta tai magana, ina ta kallon Nana kamin na maida dubana gurin Nurse din yadda ta saka tufafinta da yadda take aikinta sai ya burgeni daman na dade ina ganin sha’awar aikin likita ko unguwar zoma amman ba ni da wannan halin hali saboda ba ni da wannan gatan na karatu, wa na ke da shi da zai tsaya min nai karatu har na kai ga zama nurses ko likita? Ni da karatun secondary ma ya gagareni sai bara da aikin titi.

Bayan ta fice na zauna a kujerar dake facing dinta Lukman kuma yai kwance kasa yana jin bachi, ido na kura mata tun ina kallonta da kyau har bachi ya soma sata na, shigowar likitan ce tasa na Nana tana bude idonta tana rufewa kamar bata san inda take ba. Ni nai saurin mikewa tsaye likitan kuma yai saurin karasowa kusa da ita ya shiga dubata sai na ga yana ta murmushi.

 

“Masha-Allah tiyata ta yi kyau, na sunanta?”

 

“Nana”

 

Na bashi amsa ina wani irin murmushi da ke bayyana irin farincikin da ke raina. Sai ya shiga kiran sunanta cikin ikon Allah da iyawarsa ta amsa muryarta can kasa kasa.

 

“Na’am”

 

“Sannu”

 

Ya ce da ita a lokacin da ta kalleshi. Sannan ni ma na fada.

 

“Sannu Nana”

 

Sai ta kalleni ta gyada min kai sai kuma ya dan dago kan kadan ta kalli cikinta da ke lullube da zane.

 

“Ina Lukman”

 

“Gashi yana bachi”

 

Na bata amsa da sauri.

 

“Waya kawo ni asibiti?”

 

“Ni na kawo ki maciji ne ya tsare ki, shine wannan likitan ya taimaka ya miki tiyata ya cire miki dafin kuma yai miki allura ya siya miki magani”

 

“Allah ya saka da alheri”

 

Ta fada daker tana kallonsa. Sai ya cire mata wasu abubuwan da ke jikinta ya kalli Lukman.

 

“Bari a samo muku abunda za ku rika kwana ko, ba ki san ana dauka cuta kasa ba da za ki bar shi ya kwanta”

 

Na yi shiru bance komai ba, shi kuma ya juya ya fice daga dakin. Be jima ba ya dawo tare da wasu masu sharar asibitin su hudu ko wannensu dauke da abubuwan bukata, tabarma ce da babban bargo da filo da kuma buta da carpet din sallah, dayan kuma abinci ne ya kawo mana. Wallahi sai na rasa da wanne baki zan yi ma likitan nan godiya da irin dawainiyar da yake da mu ko da shi ya haifi Nana iyaka kenan yadda yake kashe mana kudi sai ka ce ya sanmu.

 

“Za a kawo muku kayan tea gobe, ai kin iya gada shayi ko? Sai ki rika hada mata tana sha da fruits”

 

Ya fada bayan mutanen masu shara sun fita.

 

“Dan Allah ya sunanka?”

 

Na tambaya cike da fargabar yadda zai amsa min.

 

“Ina son na rika saka ka a addu’a ta ne idan nai, irin alherin da kake mana yayi yawa kana ta dawainiya da mu kamar ka san inda muka fito”

 

Kallo yai n wasu yan mintuna kamin ya dauke kansa tare da wani guntun numfashi ya ce.

 

“Ba komai ba sai kin min addu’a ba, Allah zai ba ni lada ai”

 

Yana fadar hakan ya juya ya fice, ni kuma na bishi da kallon kauna kauna irin ta wanda ya taimake ka a halin da kake da bukatar taimakon. A dare Nana ta dan ta6a fira da ni tana tambayar abubuwan da ke mana ina ta fada mata ita kanta tai farinciki sosai kuma tai masa addu’a sannan ta sha kankana kadan kamar yadda ya umarta, ni ko a daren sai da nai tas na ci na koshi sannan na kwanta kan shimfidar da ya kawo mana ni da Lukman, kusan sai na ce ban taba kwanciya akan wani abu mai dadi makamancin katifa ba irin yau.

Tun daga lokacin kullum Nana cikin kara samun lafiya take, ni da Lukman kuma ba mu kara zuwa bara ba, kudin daya bani tun a karon farko ma ban sake taba su ba domin komai na ke bukata yi mana yake babu abunda muke yi da kanmu tun kama daga abinci magani da duk wani abun bukata. Sai dai abu daya yake ta bani tsoro, yadda Nana ta gagara komawa daidai, motsi kadan sai ta rike kirjinsa ko gefen cikinta ta ce ciwo yake mata kuma tana yawan fadawa likitan amman sai ya ce ba wata matsala ba ce zata ji sauki nan gaba kadan. Mutanen da muka zaman arziki da su suna ta zuwa suna duba Nana, kusan sai na yi sati ban leka gida ba idan ma wanka zan yi sai na yi a bandakin da ke dakin, daman can kuma wanka ba damu na yai ba, iya kar kokarin da na ke a yanzu na tsayar da sallah a kan lokacij ne ganin bana aikin komai a nan asibitin sai zama, Nana ma ina kokarin ganin na saka ta yi duk kuwa da irin kin son taba ruwa da take ko da na zafi ne yanzu sai ta ji jikinta ya kara rashin karfi, ganin hakan yasa na samo mata kasa na koya mata taimama kamar yadda aka koyar da mu makarantar islamiya lokacin da na ke zuwa.

Kullum cikin yi ma likitan nan da ban san sunansa addu’a muke ni da Nana, yana kulawa da mu sosai, ba dan rashin lafiyar Nana da ke cikin raina ba da Allah kadai yasan kibar da zan yi akan abubuwan dadin da muke ci, sai dai Nana kan ta kasa komawa yadda take a da, walwalarta kuzarinta da kuka sakewa ta kasa yi kusan kullum sai rama take daman can ba wani jikin ne da ita sosai ba.

Wasa wasa muka kwashe wata daya a asibitin, har zaman ya fara gundirata ita kanta Nana da ke ciwon sai ta fara gajiya, kullum addu’ar Allah ya bata lafiya mu bar asibitin, kowa mamaki yadda dafin macijin ya zame mata haka ake yi, ko da yake likitan ya fada mana cewar dafin ya warke ciwon cikin cikinta ne kawai ya rage ya warke. kusan sai na saba da nurses din da ke dan shigowa duba wani lokacin amman masu sake fuska a cikin, sauran kan sai dai su yi min kallon banza, da kuma mutanen da ke zam waje harabar asibitin suna jinyar wasu, domin idan na gaji da zama cikin dakin da take sai na dauko tabarmar nai shimfida a waje ni da Lukman mu zauna, har ita wani lokacin Nurse Shukura tana fitowa da ita ta sha iska, duk a cikin Nurse din Shukuwa ta fi sake min sai dai a yadda na lura kamar shi likitan baya son shirinmu da ita, wata kila akwai rashin jituwa a tsakaninsu ne ko kuma wani abun oho, domin na lura da ita ma kamar bata jindadin yadda muke yabonsa muke saka masa albarka da addu’ar alheri.

Haka nan kawai wani lokacin idan bata aikin komai sai ta shigo dakinmu mu yi ta fara kamar mun saba, ta haka har na san unguwar da take zama wato tudun wada da kuma inda ni ma nake zama har take ce min tana da wata kawa a kusa da mu, akwai ranar da take fada min cewar tana tausayina ni da Lukman jin cewar ba mu da kowa a nan Nigeria ko ma muna da su ni ban sansu ba, domin Mahaifina be tana fada min ba Nana ma bata nuna fada min ba, har take ce min ya kamata na nemi yan’uwa ko’in suke saboda wata rana. A lokacin na samu Nana na tisata a gaba ina tambayar wasu daga cikin yan’uwanta har take fada min harma da na Babana ma.

Misalin karfe biyu da yan mintuna na fito daga dakin na nufo gurin da muke zama a harabar asibitin inda shuke-shuke na zauna. Ban yi minti hudu da zama gurin ba sai ga kawata Farida ta zo, na jidadin zuwanta domin yau harabar babu mutanen da muka saba fira wasu an sallame su wasu kuma suna ciki gurin kula da masara lafiya, wadannn bakin fuskar kuma sun tsare ni da idonsu, dukuwa da nasa wannan kallon baya rasa nasaba da irin kyauna da kuma manyan idanuwan da Allah yai min haka zalika gashin kaina, shiyasa ba kasafai na ke son yin alwala a waje ba sai gaka hankali kowa ya dawo kaina duk da kasancewar gashin nawa a cinkushe yake guri daya har wani warin tsami yake, domin ba kitso nake masa ba idan am anyi kitson sai warware saboda sulbin gashi, kuma ba damuwa nai da na wanke ba balle har na shace shi ko na gyara.

Dambun da suka na masara ne ta riko mana, duk da kasancewar bana jin yunwa amman hakan be hana ni ci ba domin ina son dambu kusan duk wani abu da za a sarrafa shi da masara ko shimkafa ko dawa ina sonsa. Na ci dambu da yawa saboda yajin da aka cika a ciki domin ni ma’abociyar cin ya ji ce sosai, bayan mun gama fira ta shiga ciki ta duba Nana tai mata ta jiki sannan ta fito na rakota har bakin titin ringin sambo ina ta jin kamar na bita dan har ga Allah zaman asibitin ya fara ci min rai. A hanyata ta dawowa ne na hadu da Nurse Shukura tana sanye da uniform dinta amman ta dora bakar abaya sama ta rataya jakarta da alama ta tashi daga aikin ne zata tafi gida.

 

“Anty Shukura kin tashi ne”

 

“Eh sai kuma gobe, na kika fito?”

 

“Wallahi kawata na raka ina jin kamar na bita, zaman asibitin nan na ishemu”

 

Na fada ina yar dariya kadan, sai tai murmushi ta ce.

 

“Zama kan ai yanzu kuka fara tunda har kika ga Doc Asim ne yake kula da ku, in ma kina son mahaifiyarku ta samu lafiya to ki dauke ta daga asibitin nan ki kaita wata ko ku koma a gida, idan ba haka ba Wallahi za ki iya rasa mahaifiyarki asibitin nan ballantana yana ganin ba ku da kowa kin ga asirinsa rufe ba wanda zai san dalilin mutuwar mahaifiyarku”

 

Hankali na tashi da ji kalamanta har ya kasa boyuwa a fuska ta.

 

“Me kike Nufi Anty Shukura?”

 

“Bana nufin komai kawai baki ganin ciwon mahaifiyarki na ki ci ya ki cinyewa kullum kuna nan, ai ya kamata ki yi tunanin canja mata asibiti, kuma karki ce ni na baki shawara idan kin tashi kawai ki ce ke kin gaji gida za ku koma, Wallahi da masu kudi ne ku ko masu yan’uwan da yanzu an yi tunanin wata hanyar daban amman ba zama haka nan ba har kuna kokarin shiga wata na biyu asibitin nan, akan saran maciji kawai haba Ataa ke ma ai ya kamata ki yi tunani”

 

Tana gama fadar hakan ta yi wucewarta ta bar ni nan tsaye ina ta nazarin maganganunta, gaskiya ta fada wani gurin tabbas da masu kudi fa yanzu an canja nata asibiti amman kuma mu ba kamar su ba ne, kuma idan muka ce za mu canja asibiti kudin magani dawainiya wa zai yi da mu? Na san dai ba za mu hadu da dan albarka likita kamar wannan ba. In ta wannan sake saken na nufi cikin ward din tare da tunanin wata kila likitan be kware sosai ba shiyasa ka Nana ta gagara warkewa garau.

 

 

About the author

mynovels

Leave a Comment